Sojojin Iran sun gwada amfani da sabbin jiragen yakin na zamani da suka kera a cikin gida, a cikin atisayen Zulfikar 1403 da ke gudana a kudancin kasar, wanda kuma ya hada rundunonin sojojin kasar daban-daban.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto majiyar atisayin na cewa sojojin sun gwada amfani da jirgin saman yaki samfurin Yak-130 a cikin atisayen.

Inda suka tabbatar da ingancinsa.

Ana gudanar da atisayen Zulfikar 1403 ne a yankin Tekun Omman da kuma wani bangare na yankin Tekun farasa daga kudancin kasar Iran.

Bugediya Janar Alireza Sheikh kakakin atisayen ya fadawa tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran kan cewa wannan bangare kadan ne daga atisayen, amma a yau sun gwada karfi da ingancin samfurin jiragen yaki yak-130 ne a karon farko kuma sun kara tabbatar da ingancisu.

Janar Sheikh ya kara da cewa wannan hotunan bidiyo da kuka ganin bangare ne na inda jirgin ya gwada korewarsa na kakkabo wani jirgi wanda ake sarrafashi daga nesa na makiya tare da amfani da garkuwan makami mai linzami samfurin MiG-29.  Sannan an ga yadda ya sami nasarar kakkabo shi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An yi garkuwa da masu ibada a Kogi

’Yan bindiga sun kai hari a kan taron masu ibada inda suka yi awon gaba da mutane da dama da ba a tantance ainihin yawansu ba.

Mutane suna tsaka da gudanar da ibadar dare ne a kan wani tsauni a lokacin da ’yan bindigar suka kai musu farmakin suka yi garkuwa da su.

Lamarin ya auku ne a ranar Juma’a yankin Egbola, a kan hanyar Agabja a Ƙaramar Hukumar Lokoja.

Shaidu sun bayyana cewa ’yan bangan gwmanatin jihar sun yi nasarar ceto wata mata daga cikin masu ibadan, bayan sun samu rahoton aukuwar lamarin.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Rikice-Rikice A Jihar Filato Yadda kisan mutum fiye da 50 a Filato ya tayar da ƙura

Wani ɗan banga daga cikin waɗanda suka kai ɗauki ya bayyana cewa matar ta tsere ne bayan da ’yan bindigar suka kawo harin, daga bisani ’yan bindigar suka tsince ta.

Wakilinmu ya yi ƙoƙarin yin magana da mai magana da yawun ’yan sanda a Jihar Kogi, ASP William Aya, amma jami’in bai amsa ko ɗaya daga cikin kiraye-kirayen wayan wakilin namu ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Yi Aiki Tare Don Daidaita Mummunan Yanayi A Yankin Manyan Tabkuna Na Afirka
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Makasudin Rubuta Sakon Jagora Ga Shugaban Kasar Rasha
  • Dangote: Har yanzu gidajen mai ba su rage farashin mai ba
  • Mizanin Hada-hadar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 5.4% A Rubu’in Farko Na Bana
  • Hamas Ta Fadawa Iyalan Yahudawan Da Take Tsare Dasu A Gaza Kan Cewa ‘Ya’yansu Zasu Koma A Cikin Akwatunan Gawaki
  • UEFA: Barcelona Ta Kai Zagayen Kusa Da Karshe A Karon Farko Cikin Shekaru 9
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
  • Jagoran Ya Ce: Iran Ba Ta Kallon Tattaunawan Iran Da Amurka A Matsayin Kawo Karshen Takaddama A Tsakaninsu
  •  Aljeriya Ta Kori Jami’an Diflomasiyya Faransa 12
  • An yi garkuwa da masu ibada a Kogi