HausaTv:
2025-02-24@21:15:48 GMT

Kungiyar Hamas Ta Dakatar Da Tattaunawa Da HKI Har Zuwa Sakin Fursinoni Falasdinawa

Published: 24th, February 2025 GMT

Kungiyar Hamas ta bada sanarwan dakatar da tattaunawa da HKI har zuwa lokacin da ta saki fursinoni Falasdinawa wadanda yakamata ta sakesu bayan da Hamas ta saki yahudawa 6 a karo na 7 na musayar fursinoni.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto daya daga cikin shuwagabannin kungiyar Mahmoud Mardawi yana fadar haka a yau Litinin ya kuma kara da cewa, a ranar Asabar da ta gabata ce kungiyar ta saki fursinoni yahudawa  6, kuma take fatan HKI za ta saki falasdinawa 620 kamar yadda yake cikin yarjeniyar tsagaita wuta, amma ta ki yin hakan, da dalilin cewa wai kungiyar Hamas ta wulakanta daya daga cikin fursinoni 6 da ta saka.

Jami’in na Hamas ya ce tawagar tattaunawar Hamas ba za ta gana da tawagar HKI don tattauna ci gaban da ke cikin yarjeniyar tsagaita wutar ba, har zuwa lokacinda HKI ta sake wadannan Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar Hizbullah Ta Lebanon Ta Jaddada Rashin Amincewarta Da Mika Kan Kasar Ga Amurka Da Haramtacciyar Kasar Isra’ila

Kungiyar Hizbullahi ta bayyana cewa: Ba su yarda kasar Lebanon ta mika kai ga haramtacciyar kasar Isra’ila da Amurka ba

Mataimakin shugaban majalisar zartaswar kungiyar Hizbullah Sheikh Ali Damoush ya jaddada cewa: Ba zasu amince kasar Lebanon, mai cin gashin kanta ta kasance karkashin dokar haramtacciyar kasar Isra’ila da Amurka a karkashin matsin lamba da barazanar kai hari kan filin jirgin saman Lebanon da sauran muhimman wuraren kasar ba.

Sheikh Damoush ya jaddada a cikin hudubarsa ta Juma’a cewa “ya zama wajibi gwamnati ta magance matsalar jiragen Iran zuwa kasar Lebanon, domin wannan batu na farko da na karshe yana da alaka ne da ‘yancin kai da kuma martabar kasar Lebanon, kuma hakan na nuni da kwace ‘yancin matakin da kasar Lebanon ta dauka. Saboda hana saukar jiragen saman Iran a filin tashi da saukar jiragen sama na birnin Beirut wani mataki ne na haramtacciyar kasar Isra’ila da Amurka, kuma hakan wani tsoma baki ne a alakar kasa da kasa ta Lebanon, kuma hakan zai bude kofar jerin bukatu da gindaya sharuddan kan batun jigilar jiragen saman Iran, kuma ba a san inda za su kare ba, sabanin muradun Lebanon da al’ummar kasar.

A wani labarin kuma, Mataimakin Shugaban Majalisar Zartarwar kungiyar Hizbullah, Sheikh Ali Damoush, ya tabbatar da cewa: An gayyace su don halartar jana’izar Sayyid Hassan Nasrallah, wannan fitaccen shugaba mai girman tarihi, a wani yanayi na musamman, mai tarihi da wayewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • IRGC Ta Bayyana Cewa Taron Jana’izar Nasarallah Ya Yi Tisara A Duniya Gaba Daya Saboda Barazanar Da Jiragen Yakin HKI Ta Yi Wa taron
  • NNPP Ta Dakatar da ‘Yan Majalisa Huɗu Bisa Zargin Yi Wa Jam’iyya Zagon Ƙasa
  • Hamas ta yaba da irin goyon bayan da Sayyed Nasrallah ya baiwa Falasdinu
  • Zan Samar da Karin Makarantu a Zaria – Dr. Abbas Tajuddeen
  • Wang Yi: Sin Za Ta Ci Gaba Da Mara Baya Ga Garambawul Na Kungiyar WTO 
  • Hamas, Da OIC Sun Yi Allawadai Da Dirar Mikiyan Da HKI Take Yi A Tulkaram Na Yankin Yamma Da Kogin Joirdan
  • Kungiyar Hizbullah Ta Lebanon Ta Jaddada Rashin Amincewarta Da Mika Kan Kasar Ga Amurka Da Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Kungiyar Hamas Zata Saki Fursunoni 6, Yayin Da’Yan Sahayoniyya  Zasu Saki Fursunonin Falasdinawa 602
  • Isra’ila-Hamas: Za’ayi Musayar Fursunonin Karshe Karkashin Yarjejeniyar Farko