HausaTv:
2025-03-28@04:00:15 GMT

Kungiyar Hamas Ta Dakatar Da Tattaunawa Da HKI Har Zuwa Sakin Fursinoni Falasdinawa

Published: 24th, February 2025 GMT

Kungiyar Hamas ta bada sanarwan dakatar da tattaunawa da HKI har zuwa lokacin da ta saki fursinoni Falasdinawa wadanda yakamata ta sakesu bayan da Hamas ta saki yahudawa 6 a karo na 7 na musayar fursinoni.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto daya daga cikin shuwagabannin kungiyar Mahmoud Mardawi yana fadar haka a yau Litinin ya kuma kara da cewa, a ranar Asabar da ta gabata ce kungiyar ta saki fursinoni yahudawa  6, kuma take fatan HKI za ta saki falasdinawa 620 kamar yadda yake cikin yarjeniyar tsagaita wuta, amma ta ki yin hakan, da dalilin cewa wai kungiyar Hamas ta wulakanta daya daga cikin fursinoni 6 da ta saka.

Jami’in na Hamas ya ce tawagar tattaunawar Hamas ba za ta gana da tawagar HKI don tattauna ci gaban da ke cikin yarjeniyar tsagaita wutar ba, har zuwa lokacinda HKI ta sake wadannan Falasdinawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar IAEA ta yi ishara da yiwuwar sake komawa teburin tattaunawa tare da Iran

Bayan gazawar tattaunawar da hukumar ta IAEA ta yi da Tehran, babban daraktan hukumar Rafael Grossi ya jaddada muhimmancin komawa kan teburin shawarwari nan gaba don tabbatar da cewa Iran ba ta mallaki makamin nukiliya ba.

Hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ta ce tattaunawar da ta yi da wani babban jami’in kasar Iran a baya-bayan nan, ba a samu wani ci gaba kadan ba a cikin binciken nukiliyar da aka shafe shekaru ana yi kan kasar Iran, yana mai jaddada bukatar gaggauta warware takaddamar diflomasiyya da ke tsakanin Tehran da Washington.

A wata hira da Bloomberg babban darektan hukumar Rafael Grossi ya tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba zai koma Tehran domin ci gaba da tattaunawa da jami’an Iran. “Muna kan wani muhimmin mataki,” in ji Grossi, yana mai cewa wadannan tattaunawa za su iya taka muhimmiyar rawa a nan gaba.

Grossi ya kara da cewa shugaban kasar Amurka Donald Trump ya aike da wasika zuwa ga jagoran ruhin Iran, wanda ke nuni da bukatar cimma fahimtar juna da ke musanta yuwuwar Iran ta mallaki makamin nukiliya.

A sa’i daya kuma, Grossi ya jaddada bukatar shugabannin kasashen duniya su yi taka-tsan-tsan da kamewa, a daidai lokacin da ake ci gaba da tafka mahawara ta kasa da kasa game da bukatar dakile makaman nukiliya.

A cikin jawabinsa, Grossi ya bayyana cewa, duniya na fuskantar kalubale guda biyu: a bangare guda, akwai batutuwan da ba a warware su daga baya ba, a daya bangaren kuma, damar da ta kunno kai na cimma wata yarjejeniya nan gaba da za ta kai ga cimma matsaya kan batun nukiliyar Iran na dogon lokaci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila ta sake kashe wani kakakin Hamas
  • Isra’ila : An yi zanga zangar adawa da gwamnatin Netanyahu a Tel-Aviv
  • Duniyarmu A Yau: Ranar Qudus Ta Duniya Ta Shekara 1446
  • Hukumar IAEA ta yi ishara da yiwuwar sake komawa teburin tattaunawa tare da Iran
  • Rasha Da Ukraine Sun Amince Da Tsagaita Wuta A Tekun Black Sea
  • Sudan: RSF ta hana kayan agaji a yankunan da ke a karkashin ikonta
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI
  • Hamas : Isra’ila ta yi amfani da sulhu wajen tattara bayanai kan shugabannin Hamas domin kashe su
  • NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 61 cikin sa’o’i 24