Leadership News Hausa:
2025-02-24@21:45:44 GMT

Kasar Sin Ta Cimma Burin Magance Gurbatar Yanayi A Shekara Ta 2024

Published: 24th, February 2025 GMT

Kasar Sin Ta Cimma Burin Magance Gurbatar Yanayi A Shekara Ta 2024

Ma’aikatar kula da muhallin halittu ta kasar Sin ta gudanar da taron manema labarai a yau Litinin 24 ga wata, inda wani jami’inta ya nuna cewa, ingancin iska da muhallin kasar sun kyautatu a shekarar da ta gabata, lamarin da ya shaida cewa, kasar Sin ta cimma burin magance gurbatar yanayi a shekara ta 2024.

Jami’in ya kara da cewa, a shekara ta 2024, yawan kwanakin da aka samu kyakkyawan ingancin iska ya kai kaso 87.2%, adadin da ya karu da kaso 1.7% idan aka kwatanta da na shekara ta 2023. Kazalika, yawan kwanakin da aka samu mummunar gurbatar yanayi ko fiye da haka, ya kai kaso 0.9%, adadin da ya ragu da kaso 0.7%. A Beijing, wato fadar mulkin kasar Sin kuma, ingancin iska ya dauki matsayin kasa na biyu cikin shekaru 4 a jere, inda har kullum a kan samu kyakkyawan yanayi. (Murtala Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya Yi Fatali Da Zargin Australia A Kan Atisayen Sojojin Kasar

Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin ya yi Allah wadai da kasar Australia bisa yadda ta zargi kasar Sin da yin atisayen soja bisa doka a tekun dake kusa da kasar ta Australia.

Kakakin, Wu Qian ya bayyana hakan yayin da yake amsa tambayoyin kafofin watsa labaru game da zargin na Australia cewa jiragen ruwan yaki uku na kasar Sin sun yi atisayen soja a tekun dake kusa da kasar Australia.

Wu Qian ya bayyana cewa, zargin da kasar Australia ta yi ba shi da tushe balle makama, domin yankin tekun da jiragen ruwan yakin na kasar Sin suka yi atisayen soja yana can nesa da layin teku na kasar Australia, kuma yanki ne da ba ya cikin mallakar wata kasa. Kakakin ya kara da cewa, kafin lokacin, sai da kasar Sin ta ba da sanarwa sau da dama a kan gudanar da atisayen, sai dai kuma abin mamaki, bayan da jiragen ruwan yakin kasar suka harba boma-bomai zuwa tekun, sai Australiya ta yi zargin.

Ya ce, Sin ta gudanar da ayyukan atisayen bisa dokokin kasa da kasa da ka’idojin zirga-zirga na kasa da kasa, wadanda ba za su kawo illa ga tsaron zirga-zirgar jiragen sama ba. Kuma kasar ta Australia ta san lamarin, amma kuma ta zargi kasar Sin da abin da ba shi da tushe balle makama, kuma Sin tana nuna rashin jin dadinta game da batun. (Zainab Zhang)

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda jama’a suka kama ɗan shekara 65 ɗauke da bindiga
  • Kakakin Ma’aikatar Tsaron Kasar Sin Ya Yi Fatali Da Zargin Australia A Kan Atisayen Sojojin Kasar
  • Sharki: Takaitaccen Rayuwar Sayyid Shahid Hassan Nasarallah (r)
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Taya Gwamna Bago Murnar Cika Shekara 51
  • Ɗan shekara 43 ya auri mai shekara 88
  • Sojojin Ruwa Da Kuma Sojijin Sama Na JMI Sun Hada Guiwa Don Yin atisaye Tare Mai taken Zulfikar
  • Kungiyar Hizbullah Ta Lebanon Ta Jaddada Rashin Amincewarta Da Mika Kan Kasar Ga Amurka Da Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Sibil Difens ta cafke mutum 17 kan aikata sata a Yobe
  • Da Ɗumi-ɗumi: Sanata Lawal Yahaya Gumau Ya Rasu Yana Da Shekara 57