Aminiya:
2025-02-24@22:45:10 GMT

Uwa ta jefo jaririnta daga saman bene mai hawa biyu

Published: 24th, February 2025 GMT

Wani jariri sabuwar haihuwa ya riga mu gidan safiyar Litinin bayan mahaifiyarsa ta jefo shi ta tagar wani otel a birnin Paris. Jami’an tsaro da ke shigar da ƙara sun ce an tsinci gawar jaririn wanda ko cibiyarsa ba a yanke ba. An yi zanga-zangar kisan ɗalibi a Jami’ar FUDMA da ke Katsina NNPP ta dakatar da Kawu Sumaila da Ali Madakin Gini Wata majiya ta ce uwar jaririn mai shekaru 18 ta jefo shi ne ta tagar ɗakin wani otel daga hawa na biyu a Kudancin Faransa.

An bai wa jaririn kulawar gaggawa amma a ƙarshe ya ce ga garinku nan kamar yadda majiyar ta tabbatar. ’Yan sanda sun ce jaririn ya mutu da misalin ƙarfe 7:45 na safiya agogon GMT a Asibitin Debre kamar yadda Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ya ruwaito.Bayanai sun ce uwar jaririn wadda ɗaliba ce ’yar asalin ƙasar Amurka ta jefo jaririn ne bayan haihuwarsa a ɗakin da ke hawa na biyu na otel ɗin

Tuni dai mahukunta a Faransa suka ƙaddamar da bincike kan lamarin yayin da suka tabbatar da cafke matashiyar da ake zargi.

An ruwaito cewa BaAmurkiyar na daga cikin tawagar wasu matasan ɗalibai da ke yawon ƙaro ilimi a nahiyar Turai.

A halin yanzu dai an kai matashiyar asibiti domin samun kulawar da ta dace a sanadiyar haihuwar da ta yi a yayin da bincike zai ci gaba da gudana.

 

AFP

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jariri Paris Uwa

এছাড়াও পড়ুন:

Hamas ta yaba da irin goyon bayan da Sayyed Nasrallah ya baiwa Falasdinu

Kungiyar Hamas ta jinjina da irin babbar gudunmawa da tsayin dakan da Sayyed Hassan Nasrallah da Sayyed Hashem Safieddine suka yi wajen goyon bayan Palastinu, da kuma shahadar da suka yi a kan wannan tafarki.

A cikin wata sanarwa da ta fitar dangane da jana’izar shahidan biyu, kungiyar Hamas ta ce, muna addu’ar Allah ya jikan su da rahama, tare da mika ta’aziyyarmu ga al’ummar kasar Labanon da dukkanin al’ummar mu Larabawa da musulmi.

Kungiyar ta tabbatar da cewa, laifuffukan Haramtacciyyar Kasar Isra’ila da kuma kisan gillar da ta yi wa shugabannin gwagwarmaya a Falasdinu, Labanon da sauran su, ba za su dakatar da tafarkinmu ba.

Har ila yau sanarwar ta bayyana matsayin shahid Sayyid Hassan Nasrallah da jajircewarsa da kuma sadaukar da kai ga al’ummar Palastinu, tare da yabawa kudurinsa na kafa wata hanya ta taimakawa da kuma goyon bayan al’ummar Gaza wajen tinkarar mummunan zaluncin yahudawan sahyoniyawan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda jama’a suka kama ɗan shekara 65 ɗauke da bindiga
  • Hamas ta yaba da irin goyon bayan da Sayyed Nasrallah ya baiwa Falasdinu
  • Fasinjoji 4 sun rasu yayin da bas ta kama da wuta a Jigawa
  • Magoya Bayan Tottenham Sun Yi Zanga-Zanga
  • Iran Ta Bukaci Hanzarta Hukunta Shugabannin ‘Yan Sahayoniyya Kan Laifukan Da Suka Aikata
  • An haifi alade mai fuskar mutum a Philippines
  • Mataimakin Firaministan Sin Ya Zanta Da Sakataren Baitulmalin Amurka
  • Ko Real Madrid za ta iya lashe Gasar Zakarun Turai bana?
  • Sojojin Faransa Sun Mika Sansanin Soji Mafi Girma Da Suka Mamaye Ga Sojojin Faransa