Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-17@11:41:54 GMT

Gwamnatin Jigawa Za Ta Horas Da Manoman Alkama A Birnin Kudu

Published: 24th, February 2025 GMT

Gwamnatin Jigawa Za Ta Horas Da Manoman Alkama A Birnin Kudu

Gwamnatin Jihar Jigawa ta  yi alkawarin horar da matasa da ke aikin noman alkama a karamar hukumar Birnin Kudu.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana haka yayin da ya kai ziyarar duba gonakin alkama a yankin.

Ya yabawa Shugaban karamar hukumar Birnin Kudu, Dr Muhammad Uba Builder bisa wannan shiri da ya bayyana a matsayin wata hanya ta samar da aikin yi ga matasa da bunkasa harkar noma.

Kazalika, a yayin ziyarar gani da ido, Malam Umar Namadi ya kuma ba da umarnin gaggauta gina katanga da kuma gina ofishin jami’an tsaro a sabuwar tashar bada ruwan sha mai amfani da hasken rana ta garin Birnin Kudu.

Kwamishinan Albarkatun Ruwa na Jihar, Alhaji Ibrahim Garba Hannun Giwa, ya shaida wa Gwamnan cewar, an haka rijiyoyi goma sha bakwai a wurin.

A nasa jawabin, Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu, Alhaji Muhammad Uba Builder, ya bayyana cewa Karamar Hukumar ta dauki matasa kimanin 170 don yin noman alkama.

Builder, ya ce daukar matasan na da nasaba da tallafawa kokarin gwamnatin jihar na tabbatar da wadatar abinci da bunkasar tattalin arzikin al’umma.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato

Shugaba Bola Tinubu ya bayyana bakin cikinsa kan harin da aka kai  Jihar Filato wanda ya yi sanadin mutuwar mutane fiye da 40.

A cikin wata sanarwa, Shugaban kasa ya la’anci wannan tashin hankali tare da mika ta’aziyyarsa ga Gwamna Caleb Mutfwang, Gwamnatin Jihar, da al’ummar Filato.

Sanarwar da Mai ba Shugaban Kasa shawara na musamman kan Harkokin Yada Labarai Mista Bayo Onanuga, ya sanya wa hannu, ta bukaci Gwamnan da ya nuna cikakken ikonsa wajen warware rikicin da tabbatar da zaman lafiya mai dorewa.

Shugaba Tinubu ya jaddada muhimmancin soyayya da hadin kai a maimakon  bambancin addini da kabila.

Ya bukaci shugabannin al’umma, da na addinai, da ma na siyasa a ciki da wajen jihar, da su hada kai domin kawo karshen ramuwar gayya da rikice-rikicen da suka jima suna addabar al’umma.

“Ya zaman wajibi a kawo karshen rikicin da ke faruwa tsakanin al’umma a Jihar Filato wanda ya samo asali daga rashin fahimta tsakanin kabilu da addinai daban-daban.” In ji Shugaba Tinubu.

“Na umarci hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike kan wannan rikici, da gano wadanda ke da hannu a shirya wadannan ayyukan tashin hankali. Ba za mu amince da wannan barna da hare-haren ramuwar gayya ba. Ya isa haka.

Ya ce Gwamnatin Tarayya za ta ci gaba da ba Gwamna Mutfwang da Gwamnatin Jihar Filato goyon baya wajen karfafa tattaunawa, inganta zaman tare, da tabbatar da adalci don magance wannan rikici har abada.

 

Daga Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Taron Ƙarawa Ma’aikatan Jinƙai Sani A Jihar Kano
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Garambawul A Fannin Kiwon Lafiya
  • Araghchi: babu tattaunawa kan batun tace sinadarin uranium
  • Hajj 2025: Hukumar Alhazai Ta Shirya Taron Bita Ga Mahajjata a Jihar Kwara
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
  • Rasha Ta Sanar Da Kashe Manyan Kwamandojin Sojin Ukraine Fiye Da 60 A Birnin Sumy Na Kasar Ta Ukraine
  • Al’ummar Babura Sun Karrama Sabon Shugaban Asibitin Koyarwa Na Rasheed Shekoni
  • Kwamishinan ‘Yansandan Kano Ya Nemi Taimakon Sarakunan Gargajiya Wajen Kawo Ƙarshen Faɗan Daba A Jihar
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato