Sin Ta Mai Da Martani Kan Takardar Bayani a Kan Manufar “Zuba Jari A Amurka Ta Zamanto Farko”
Published: 24th, February 2025 GMT
Mai magana da yawun kwamitin sa kaimi ga cinikayya tsakanin Sin da ketare ya amsa tambaya da manema labarai suka gabatar masa kan takardar bayani a kan manufar “Zuba jari a Amurka ta zamanto farko” a gun taron manema labarai da aka gudanar a jiya Lahadi. Inda ya ce, bangaren masana’antu da kasuwancin Sin na matukar kin yarda da matakin da Amurka ta dauka, wanda ya yi gamin-gambiza da batun tsaron kasa wuri guda, sannan ya yi hannu riga kwata-kwata da tsarin kasuwanci tsakanin kasashen biyu.
Kakakin ya kara da cewa, Amurka ta tsaurara matakan tsaro da nufin fakewa da guzuma ta harbi karsana a kan shigo da jari daga bangaren Sin a fannin kimiyya da manyan ababen rayuwa da kiwon lafiya da aikin gona da makamashi da kayayyakin da ake sarrafawa da sauransu, a hannu guda kuwa, ta yi yunkurin habaka takaita zuba jarinta a kasar Sin ta hanyar daukar matakan sanya takunkumi da tantance harkar kudade da sauransu. Kuma da zarar an aiwatar da matakan da ake dauka, za su kara tagayyara manufofin da kamfanoni za su aiwatar, zai yi matukar illa ga zaman oda da dokar cinikayyar duniya da haifar da rashin tabbaci ga tsarin samar da kayayyaki a duniya.
Kakakin ya ce, “Sin na kalubalantar Amurka da ta mutunta ka’idar kasuwanci da yin takara daidai wa daida, da kuma fahimtar ainihin iyakar batun tsaron kasar da soke kayyade zuba jari tsakanin kasashen biyu ta yadda za a shimfida yanayi mai yakini ga masana’antu da kasuwancin kasahen biyu kan hadin gwiwarsu ta moriyar juna.” (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
An kama mataimakin shugaban Sudan ta Kudu
An kama mataimakin shugaban ƙasa na farko a Sudan ta Kudu Riek Machar a babban birnin ƙasar Juba, a yayin da ake ci gaba da samun ƙaruwar zaman tankiya tsakaninsa da Shugaba Salva Kiir.
Faɗa tsakanin dakarun da ke goya wa shugabannin biyu baya ya tsananta a yankunan Rejaf da ke kudancin Juba da Wunaliet da ke yammaci.
Rahotanni sun bayyana cewa an kama shi ne tare da uwargidansa Angekina Teny.
Ana samun fargabar cewa kama shi zai iya kawo tarnaƙi ga yarjejeniyar zaman lafiya ta ƙasar.
Kama Machar na zuwa ne bayan shafe makonni ana samun tashe tashe hankula bayan shugaba Kiir ya tsare wasu daga cikin abokan Machar a farkon watan nan.
Tawagar majalisar ɗinkin duniya da ke Sudan ta Kudu tayi gargaɗin cewa ƙasar na cikin barazanar sake faɗawa cikin yaƙi, inda ta buƙaci ɓangarorin biyu suyi aiki da yarjejeniyar zaman lafiya ta 2018.