Aminiya:
2025-03-28@03:32:20 GMT

Luwaɗi: An yanke wa ɗalibai biyu hukuncin bulala a bainar jama’a

Published: 25th, February 2025 GMT

Wata kotu a lardin Aceh da ke ƙasar Indonesia ta yanke wa wasu ɗalibai maza biyu hukuncin bulala a bainar jama’a.

A ranar Litinin ce kotun ta yanke wa mutanen biyu hukuncin bayan samun su da laifin luwaɗi da juna.

Uwa ta jefo jaririnta daga saman bene mai hawa biyu An yi zanga-zangar kisan ɗalibi a Jami’ar FUDMA da ke Katsina

A yayin da mu’amala tsakanin jinsi ɗaya ta halasta a wasu yankunan ƙasar mafi rinjayen musulmi a duniya, sai ɗabi’ar ta haramta a lardin Aceh da aka ayyana dokokin shari’ar Musulunci.

Tun a watan Nuwamban bara ne dai ’yan sanda masu ɗabbaka shari’a suka kama mazajen biyu da ke karatu a wata jami’a suna aikata wannan alfasha a wani ɗaki da suka kama haya a birnin Banda Aceh.

Jami’i mai shigar da ƙara mai suna Alfian ya ce Kotun Shari’a ta Banda Aceh ta samu mutanen biyu da laifin luwaɗi kamar yadda Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ya ruwaito.

Kotun ta yanke wa ɗaya daga cikinsu bulala 85 saboda shi ne ja gaba wajen kama hayar ɗakin yayin da ta yanke wa ɗayan hukuncin bulalai 80 a cewar Alfian.

Alfian ya ce za a zartar da hukuncin yi wa ɗaliban biyu bulala gabani ko bayan watan Azumin Ramadana.

Zartar da hukuncin bulala a bainar jama’a ba sabon lamari ba ne a lardin Aceh kan laifukan da suka haɗa da caca, shan barasa ko zina.

Ƙungiyoyin kare haƙƙin bil Adama na adawa da hukuncin bulala a bainar jama’a da suke ɗauka a matsayin zalunci, sai dai wannan doka karɓaɓɓiya ce a wurin mazauna lardin Aceh.

A shekarar 2021 ce aka yi wa wasu ma’aurata masu auren jinsi bulala.

Haka kuma, a watan Janairun da ya gabata ne aka yi wa wasu maza huɗu bulala saboda caca a yanar gizo, hukuncin da shi ne na farko da aka zartar bana.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hukuncin bulala a bainar jama a a lardin Aceh ta yanke wa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa

Wasu mutane huɗu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne sun mutu a sakamakon hatsarin mota a Jihar Nasarawa.

Kakakin rundunar ‘yan sanda jihar SP Nansel Rahman, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa, inda ya ce lamarin ya auku ne lokacin da ‘yan fashin ke ƙoƙarin tserewa jami’an.

Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati

“A ranar 25 ga watan Maris ne rundunarmu ta samu wani kiran gaggawa kan wasu ‘yan fashi na tsaka da ta’asa a bayan filin wasa na ƙaramar hukumar Keffi.

“Bayan samun kiran ne kwamishinan ‘yan sanda Shettima Jauro Mohammed ya ba da umarnin bin bayan ‘yan fashin nan take.

“Suna cikin guje mana ne a cikin motar da suka sace ƙirar Toyota Camry suka yi haɗari a babban titin Abuja-Keffi.

“Jami’anmu da ke ofishin ‘yan sanda na Goshen ne suka kwashe su zuwa asibiti, a nan mutum huɗu suka mutu.

“Ɗayan da ya rage kuma na hannunmu likitoci na bashi kulawa.

Binciken ‘yan sanda dai ya kai ga gano wasu kayan da ‘yan fashin suka sata da suka haɗa wayoyin hannu 12, agogunan hannu, sai makamai da suka haɗa da manyan wuƙaƙe biyu, sukundireba, da kuma layu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arzikin Duniya
  • Majalisa ta janye ƙudirin tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma
  • Gobara Ta Ƙone Sabon Ginin Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Mata Na Jami’ar Sokoto 
  • An kama mataimakin shugaban Sudan ta Kudu
  • Kwara Ta Gargadi Jama’a Akan Gine-Gine Akan Bututun Ruwa
  •  Nigeria: An  Kashe Sojoji Da DAma A Wani Hari Da Aka Kai Wa Sansanonin Soja Biyu Hari A Jihar Borno
  • Jagoran Juyin Musulunci Ya Amince Da Yin Afuwa Ga Wasu Fursunoni Masu Yawa
  • ’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa
  • Rikicin Masarauta: Duk mai ja da hukuncin Allah ba zai yi nasara ba — Sanusi II
  • ECOWAS Za Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa