Luwaɗi: An yanke wa ɗalibai biyu hukuncin bulala a bainar jama’a
Published: 25th, February 2025 GMT
Wata kotu a lardin Aceh da ke ƙasar Indonesia ta yanke wa wasu ɗalibai maza biyu hukuncin bulala a bainar jama’a.
A ranar Litinin ce kotun ta yanke wa mutanen biyu hukuncin bayan samun su da laifin luwaɗi da juna.
Uwa ta jefo jaririnta daga saman bene mai hawa biyu An yi zanga-zangar kisan ɗalibi a Jami’ar FUDMA da ke KatsinaA yayin da mu’amala tsakanin jinsi ɗaya ta halasta a wasu yankunan ƙasar mafi rinjayen musulmi a duniya, sai ɗabi’ar ta haramta a lardin Aceh da aka ayyana dokokin shari’ar Musulunci.
Tun a watan Nuwamban bara ne dai ’yan sanda masu ɗabbaka shari’a suka kama mazajen biyu da ke karatu a wata jami’a suna aikata wannan alfasha a wani ɗaki da suka kama haya a birnin Banda Aceh.
Jami’i mai shigar da ƙara mai suna Alfian ya ce Kotun Shari’a ta Banda Aceh ta samu mutanen biyu da laifin luwaɗi kamar yadda Kamfanin Dillancin Labaran Faransa AFP ya ruwaito.
Kotun ta yanke wa ɗaya daga cikinsu bulala 85 saboda shi ne ja gaba wajen kama hayar ɗakin yayin da ta yanke wa ɗayan hukuncin bulalai 80 a cewar Alfian.
Alfian ya ce za a zartar da hukuncin yi wa ɗaliban biyu bulala gabani ko bayan watan Azumin Ramadana.
Zartar da hukuncin bulala a bainar jama’a ba sabon lamari ba ne a lardin Aceh kan laifukan da suka haɗa da caca, shan barasa ko zina.
Ƙungiyoyin kare haƙƙin bil Adama na adawa da hukuncin bulala a bainar jama’a da suke ɗauka a matsayin zalunci, sai dai wannan doka karɓaɓɓiya ce a wurin mazauna lardin Aceh.
A shekarar 2021 ce aka yi wa wasu ma’aurata masu auren jinsi bulala.
Haka kuma, a watan Janairun da ya gabata ne aka yi wa wasu maza huɗu bulala saboda caca a yanar gizo, hukuncin da shi ne na farko da aka zartar bana.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hukuncin bulala a bainar jama a a lardin Aceh ta yanke wa
এছাড়াও পড়ুন:
Gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a Borno
Wata gobara ta tashi a ƙauyen Bukar da ke Ƙaramar Hukumar Konduga a Jihar Borno, ta yi ɓarna mai tarin yawa.
Gobarar ta lalata gidaje, amfanin gona, da dabbobi na miliyoyin Naira, amma babu wanda ya rasa ransa.
’Yan bindiga sun harbe fasto, sun sace wasu a coci Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — AtaWani mazaunin ƙauyen ya ce gobarar ta fara ne daga wutar girki a wani gida, sai iska mai ƙarfi ta bazata zuwa wasu gidaje, lamarin da ya sa mutane suka kasa shawo kanta.
Bayan kamawar wutar, sojojin Najeriya da ke yankin sun garzaya domin kai ɗauki.
Sun taimaka wajen kashe wutar tare da ceton tsofaffi da yara.
Kazalika, gobarar ta cinye wani ɓangare na kasuwar ƙauyen, inda ta ƙone shaguna da rumfunan abinci.
Mazauna ƙauyen sun ce yanayin iskar da ake yi a lokacin ya ƙara ta’azzara gobarar, hakan ya sa aka wahala wajen kashe ta.
Duk da hatsarin da ke tattare da wutar, sojoji sun taimaka wajen daƙile gobarar, wanda ya hana ta bazuwa zuwa wasu wurare, ciki har da makarantar ƙauyen.
Shugabannin yankin sun nuna godiyarsu ga sojojin da suka kawo musu ɗauki cikin gaggawa.
“Ba don taimakon Allah da na sojoji ba, gobarar na iya haddasa asarar rayuka,” in ji wani mazaunin ƙauyen, Bukar Usman.
A halin yanzu, Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Borno (SEMA), ta tura tawaga domin tantance asaea tare da raba kayan agaji ga waɗanda gobarar ta shafa.