Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya bukaci wadanda suka ci gajiyar shirin bayar da tallafi a mazabun  jihar da su yi amfani da damar da suka samu domin dogaro da kai.

Ya bayyana hakan ne a wajen kaddamar da shirin da majalisar da ke wakiltar mazabar Kaugama ya yi.

Malam Umar Namadi wanda ya samu wakilcin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Jigawa, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin, ya ce shirin samar da tallafin a mazabu zai kara inganta manufofi 12 na gwamnatin jihar wadanda suka hada da karfafawa al’umma don bunkasa zamantakewa da tattalin arziki a kowane mataki.

Ya yi fatan wannan karimcin zai yi kyakkyawan tasiri ga mutane  1,200 da suka ci gajiyar tallafin.

A jawabinsa, dan majalisa mai wakiltar mazabar Kaugama a majalisar dokokin jihar Jigawa, Alhaji Sani Sale Zaburan, ya yabawa gwamna Umar Namadi bisa dimbin ayyuka da shirye-shiryen da aka aiwatar a karamar hukumar Kaugama.

A cewarsa, an ware sama da naira miliyan 30 domin gudanar da shirin kuma wadanda suka ci gajiyar shirin sun hada da kananan ‘yan kasuwa, masu karamin karfi da dai sauransu.

A jawabin maraba shugaban karamar hukumar Kaugama Alhaji Usman Masaki Dansule ya yabawa bangaren zartaswa da na majalisa bisa yadda suka fara shirin ,wanda zai ci gaba da bunkasa tattalin arzikin al’umma da ke karkara.

Don haka Dansule ya bukaci wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da kudaden don inganta rayuwarsu.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa da suka ci gajiyar wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

Fursunoni 12 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Jihar Kogi

Gwamnatin jihar ta yi kira ga al’umma da su ba da hadin kai ga jami’an tsaro ta hanyar bayar da bayanai da za su taimaka wajen kamo sauran fursunonin da suka tsere.

Haka kuma, an buƙaci dangin waɗanda suka tsere da su mika kansu ga hukuma domin guje wa hukunci mai tsanani.

Wannan ba shi ne karo na farko da ake samun irin wannan matsala ba, domin a baya an samu fursunoni sun tsere daga gidajen yari daban-daban a Nijeriya.

Hakan na nuni da buƙatar ƙara tsaurara matakan tsaro a gidajen gyaran hali domin hana faruwar irin haka a gaba.

A halin yanzu, jami’an tsaro na ci gaba da bincike tare da ƙoƙarin kamo sauran fursunonin da suka tsere domin tabbatar da tsaro da zaman lafiya a yankin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Na Adawa Da Kara Yawan Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Amurka Ta Takaita Fitar Da Kayayyakinsu
  • Za a Fara Cin Moriyar Shirin BEAR III Na UNESCO da Koria Ta Kudu Jihar Kano
  • Ranar Quds : Hamas ta bukaci masu huduba su sadaukar da jawabansu kan Falastinu
  • Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe
  • Duniyarmu A Yau: Ranar Qudus Ta Duniya Ta Shekara 1446
  • JIBWIS Ta Raba Kayan Abinci Na Kimanin Naira Miliyan 9 Ga Marayu
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro
  • NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
  • Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD
  • Fursunoni 12 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Jihar Kogi