Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya bukaci wadanda suka ci gajiyar shirin bayar da tallafi a mazabun  jihar da su yi amfani da damar da suka samu domin dogaro da kai.

Ya bayyana hakan ne a wajen kaddamar da shirin da majalisar da ke wakiltar mazabar Kaugama ya yi.

Malam Umar Namadi wanda ya samu wakilcin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Jigawa, Alhaji Haruna Aliyu Dangyatin, ya ce shirin samar da tallafin a mazabu zai kara inganta manufofi 12 na gwamnatin jihar wadanda suka hada da karfafawa al’umma don bunkasa zamantakewa da tattalin arziki a kowane mataki.

Ya yi fatan wannan karimcin zai yi kyakkyawan tasiri ga mutane  1,200 da suka ci gajiyar tallafin.

A jawabinsa, dan majalisa mai wakiltar mazabar Kaugama a majalisar dokokin jihar Jigawa, Alhaji Sani Sale Zaburan, ya yabawa gwamna Umar Namadi bisa dimbin ayyuka da shirye-shiryen da aka aiwatar a karamar hukumar Kaugama.

A cewarsa, an ware sama da naira miliyan 30 domin gudanar da shirin kuma wadanda suka ci gajiyar shirin sun hada da kananan ‘yan kasuwa, masu karamin karfi da dai sauransu.

A jawabin maraba shugaban karamar hukumar Kaugama Alhaji Usman Masaki Dansule ya yabawa bangaren zartaswa da na majalisa bisa yadda suka fara shirin ,wanda zai ci gaba da bunkasa tattalin arzikin al’umma da ke karkara.

Don haka Dansule ya bukaci wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da kudaden don inganta rayuwarsu.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa da suka ci gajiyar wadanda suka

এছাড়াও পড়ুন:

Lauyoyin London Suna Tattara Bayanai Kan ‘Yan Birtaniya Da Suka Yi  Yaki Cikin Sahun Yahudawan Sahayoniyya A Gaza

Lauyoyin Landan suna tattara bayanai kan ‘yan Birtaniya da suka yi aiki a cikin rundunar sojojin mamayar Isra’ila

Kwararru kan harkokin shari’a na kasar Biritaniya sun ce gurfanar da wasu ‘yan kasar masu takardar ‘yan kasa biyu da ke aiki a cikin sojojin mamayar Isra’ila a gaban kuliya bisa zargin hannu a tafka laifukan yaki a Gaza, zai yi tasiri ga wadanda ke tunanin shiga cikin sahunsu.

Hakan ya biyo bayan gabatar da rahoto ga rundunar ‘yan sandan birnin Landan ne mai kunshe da shaidun da suka shafi ‘yan Birtaniya guda 10 da suka yi aikin soja karkashin rundunar mamayar haramtacciyar kasar Isra’ila da ake zargi da aikata laifukan yaki a Gaza.

A cewar wani rahoto da kamfanin dillancin labarai na Anadolu ya wallafa, lauyoyin cibiyar kare hakkin jama’a da cibiyar kare hakkin bil’adama ta Falasdinu sun gabatar da rahoto ga sashin yaki da ta’addanci na ‘yan sandan birnin London, wanda kuma ke binciken laifukan yaki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Garambawul A Fannin Kiwon Lafiya
  • An Watsa Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Masu Jan Hankalin Xi Jinping” A Kasar Malaysia
  • Jigawa Za Ta Zama Cibiyar Binciken Lafiya Nan Ba Da Jimawa Ba – Gwamna Namadi
  • Amurka Tana Shirin Mikawa HKI Dubban Boma-Bomai Cikin Makonni Masu Zuwa
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
  • Lauyoyin London Suna Tattara Bayanai Kan ‘Yan Birtaniya Da Suka Yi  Yaki Cikin Sahun Yahudawan Sahayoniyya A Gaza
  • An Kashe Sojojin Yahudawa A Gaza A Yayinda Wasu Da Dam Suka Ji Rauni
  • An yi garkuwa da masu ibada a Kogi
  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe