Ya Kamata Trump Ya Yi Koyi Da Nixon
Published: 25th, February 2025 GMT
Ranar 21 ga watan Fabrairu ne aka cika shekaru 53 da shugaban kasar Amurka na lokacin Richard Nixon ya kawo ziyara kasar Sin a shekara ta 1972, ziyarar ta sauya tarihin duniya, ta kuma samar da tushen ci gaban yankin Asiya da tekun Pasifik cikin lumana. Lokacin da tunanin yakin cacar baka ya yi kamari a Amurka, Nixon ya fahimci muhimmancin jamhuriyar jama’ar kasar Sin a ci gaban Asiya da duniya baki daya.
Duk da cewa, akwai da yawa daga cikin kalaman Trump dake nuna yakininsa na cewa zai iya “sassantawa” da kasar Sin da kuma yabon da yake yi wa shugaban kasar Sin Xi Jinping, za a iya samun wata boyayyar ajanda karkashin manufar Trump fiye da kallon kasar Sin a matsayin “kishiya ko abokiyar takara”. To, idan duk harajin da ya yi barazanar kakabawa suka fara aiki, ba shakka matakin zai yi tasiri ga tattalin arzikin kasar Sin, amma zai fi yin tasiri ga mabukatan Amurka. Wasu na ganin zai iya haifar da koma bayan tattalin arziki a duniya. Kana, zai yi matukar wahala a kai ga cimma matsaya da fahimtar juna wajen tunkarar dabaru ko wasu batutuwa masu muhimmanci a tsakanin kasashen biyu idan har aka fara gasar daukar matakan da za su illata tattalin arziki. Gaskiyar lamarin ita ce, farfado da tattalin arzikin Amurka kamar yadda Trump ya yi ikirari na bukatar karin zuba jari a ababen more rayuwa na Amurka da kuma kokarin hadin gwiwa daga bangaren gwamnatin Amurka don habaka fannin kimiyya da fasaha, sai dai kash, babu dayan wadannan da ke faruwa a halin yanzu. Maslaha mafi sauri da sauki ita ce yin aiki da kasar Sin kamar yadda Nixon ya yi, ba yin adawa da ita ba. Amma fa da Trump zai gane. (Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Trump ya yi
এছাড়াও পড়ুন:
Yake-Yaken Kasa Da Kasa Ne Suka Mamaye Taron G20 Na Ministocin Harkokin Wajen Kungiyar A Afirka Ta Kudu
A jiya Jumma’a ce aka kammala taron kungiyar kasashen G20 a birnin johanasboug na kasar Afrika ta Kudu, kuma inda batun yake-yake a yankunan daban-daban na duniya ne suka mamaye taron.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa yakin Ukraine da Rasha Hamas da HKI, Congo da sauransu ne suka mamaye taron inda ministocin harkokin wajen kasashen na G20 suka tattauna a kansu.
Ministan harkokin wajen na kasar Afrika ta Kudu Ronal Ramola ya bayyana cewa duk tare da cewa babu wani babban jami’an gwamnatin kasar Amurka a taron amma taron ya gudana kamar yadda ake saba.
Kungiyar G20 Taron kasashe masu arziki a duniya, wadanda suke da kasha 85% na tattalin arziki a duniya sannan suna da kasha 3/4 na harkokin kasuwanci a duniya.
Wannan ne karon farko wanda aka gudanar da taron a nahiyar afrrika, kuma a cikin watan Nuwamba na wannan shekaran ne za’a gudanar da taron shuwagabannin kasashen sannan Amurka ce zata karbi shugabancin kungiyar daga hannun afirka ta kudu.