Leadership News Hausa:
2025-04-18@04:17:14 GMT

Ya Kamata Trump Ya Yi Koyi Da Nixon

Published: 25th, February 2025 GMT

Ya Kamata Trump Ya Yi Koyi Da Nixon

Ranar 21 ga watan Fabrairu ne aka cika shekaru 53 da shugaban kasar Amurka na lokacin Richard Nixon ya kawo ziyara kasar Sin a shekara ta 1972, ziyarar ta sauya tarihin duniya, ta kuma samar da tushen ci gaban yankin Asiya da tekun Pasifik cikin lumana. Lokacin da tunanin yakin cacar baka ya yi kamari a Amurka, Nixon ya fahimci muhimmancin jamhuriyar jama’ar kasar Sin a ci gaban Asiya da duniya baki daya.

Nixon, ya kasance dan siyasa mai ra’ayin mazan jiya wanda ya girma cikin yakin cacar baka, amma duk da haka ya keta shingayen mulkin mallaka, danniya da babakere na wancan lokaci don fahimta da sauke alhakin da ke kansa na tarihi, ta hanyar hadin gwiwa da tuntuba, wanda ya dace shugaban Amurka mai ci Donald Trump ya yi koyi daga gare shi. Sai dai shi Trump ya zabi barazana da sa-in-sa a matsayin hanyar sadarwarsa. Karin harajin kashi 25 kan karafa da goron ruwa da Trump ya yi barazana, da karin harajin kashi 10 da ya dorawa kayayyakin kasar Sin, mataki ne da ya yi watsi da ruhin dangantaka da Nixon ya shimfida, ya kuma karya lagon alakar Amurka da Sin. Bugu da kari, da dama daga cikin sanannun “masu adawa da kasar Sin” sun samu gindin zama a gwamnatin Trump.

Duk da cewa, akwai da yawa daga cikin kalaman Trump dake nuna yakininsa na cewa zai iya “sassantawa” da kasar Sin da kuma yabon da yake yi wa shugaban kasar Sin Xi Jinping, za a iya samun wata boyayyar ajanda karkashin manufar Trump fiye da kallon kasar Sin a matsayin “kishiya ko abokiyar takara”. To, idan duk harajin da ya yi barazanar kakabawa suka fara aiki, ba shakka matakin zai yi tasiri ga tattalin arzikin kasar Sin, amma zai fi yin tasiri ga mabukatan Amurka. Wasu na ganin zai iya haifar da koma bayan tattalin arziki a duniya. Kana, zai yi matukar wahala a kai ga cimma matsaya da fahimtar juna wajen tunkarar dabaru ko wasu batutuwa masu muhimmanci a tsakanin kasashen biyu idan har aka fara gasar daukar matakan da za su illata tattalin arziki. Gaskiyar lamarin ita ce, farfado da tattalin arzikin Amurka kamar yadda Trump ya yi ikirari na bukatar karin zuba jari a ababen more rayuwa na Amurka da kuma kokarin hadin gwiwa daga bangaren gwamnatin Amurka don habaka fannin kimiyya da fasaha, sai dai kash, babu dayan wadannan da ke faruwa a halin yanzu. Maslaha mafi sauri da sauki ita ce yin aiki da kasar Sin kamar yadda Nixon ya yi, ba yin adawa da ita ba. Amma fa da Trump zai gane. (Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Trump ya yi

এছাড়াও পড়ুন:

An Yi Kira Ga Jihohi Da Su Kara Samar Da Ingantacciyar Hanyar Kiyon Lafiya

An bukaci gwamnatocin jihohi da su kara samar da tsarin kula da kiwon lafiya na bai daya (UHC) ga ‘yan kasa domin tabbatar da samar da ingantaccen kiwon lafiya a kasar.

 

Jami’ar Ayyuka, Kula da Lafiya ta Duniya ga Mata a Lafiya ta Duniya, Najeriya (WGH), Dokta Sienne Oluwatosin Orogun, ta yi wannan kiran a wani taro mai taken “Amfani da Dabaru da Tsarin Gida don Haɓaka Tsarin Kiwon Lafiyar Duniya” a Ilorin, jihar Kwara.

 

A cewarta akwai tsare-tsare da aka tsara don samar da inshorar lafiya mai araha ga masu rauni a cikin al’umma, ta kara da cewa aiwatar da ingantaccen aiki ya kasance kalubale.

 

Tun da farko a nata jawabin, kwamishiniyar lafiya ta jihar Kwara, Dokta Amina El-Imam, ta jaddada cewa hukumar kula da lafiya ta duniya (UHC) ita ce manufar tabbatar da cewa dukkan mutane sun samu cikakkiyar kulawar kiwon lafiya da suke bukata ba tare da fuskantar matsalar kudi ba.

 

Dokta El-Imam ya nuna damuwarsa kan kalubale kamar matsalolin kudade da karancin ma’aikata.

 

Ta ci gaba da cewa gwamnatin jihar na kokarin ganin an cimma kashi 15 cikin 100 na kasafin kudin jihar a fannin kiwon lafiya, da inganta iya aiki da kuma rike hannun mafi kyawu a cikin bukatun duniya.

 

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Yi Aiki Tare Don Daidaita Mummunan Yanayi A Yankin Manyan Tabkuna Na Afirka
  • An Kashe Mutane Fiye Da 300 A Wani Kazamin Fada A Yankin Darfur Da Ke Yammacin Kasar Sudan
  • Iraki Ce Zata Amfana Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka: Inji Sayyed Ammar Hakim
  • An Yi Kira Ga Jihohi Da Su Kara Samar Da Ingantacciyar Hanyar Kiyon Lafiya
  • WTO Ta Yi Gargadi Akan Karin Kudin Fito Na Amurka
  • Batawa Sin Suna Ba Zai Taimaka Kawar Da Tambarin Amurka A Matsayin Daular Kutsen Intanet Ba
  • Amurka Tana Shirin Mikawa HKI Dubban Boma-Bomai Cikin Makonni Masu Zuwa
  • Amurka, Ki Fahimci Cewa “Girma Da Arziki Ke Sa A Ja Bajimin Sa Da Zaren Abawa”
  • Kokarin Da Iran Take A Tattaunawa Da Amurka Shi Ne Dage Mata Takunkuman Zaluncin Da Aka Dora Mata
  • Ministan Harkokin Noma Na Kasar Iran Ya Kama Hanya Zuwa Kasar Brazil