Kasashen Kawancen Sahel Sun Kadaddamar Da Tutar Kungiyar
Published: 25th, February 2025 GMT
Kasashen nan guda uku mambobin kungiyar kawancen Sahel (AES) da suka balle daga kungiyar ECOWAS, sun kaddamar da tutarsu ta bai daya.
An kadaddamar da tutar ne a yayin haduwar ministocin harkokin wajen kasashen jiya Asabar a Bamako babban birnin kasar Mali mai rike da shugabancin kungiyar na farko.
Firaministan Mali, Janar Abdoulaye Maïga ya bayyana a yayin bikin, cewa “Tutar kungiyar AES, launin kore, tana dauke da tambarin kungiyar a tsakiyarta.
Ya jaddada cewa launin kore yana nuna alamar bege da wadata, wanda ke wakiltar dukiya da karfin tattalin arziki.
Wannan sabuwar alamar ta kunshi hadin kai da muradin bai daya na kasashen uku, inda suka kuduri aniyar yin aiki tare domin bunkasa tattalin arziki da zamantakewar yankin inji shi.
Kaddamar da wannan tuta na zuwa ne kasa da wata guda bayan da aka kaddamar da fasfo din kungiyar a ranar 29 ga watan Janairun 2025, Da nufin karfafa hadin gwiwarsu da saukaka zirga-zirgar jama’a da kayayyaki cikin ‘yanci a cikin yankin.
Wannan taron, wanda wani bangare ne na taron ministocin da ke ci gaba da gudana har zuwa ranar 23 ga watan Fabrairu, ya tabbatar da aniyar Mali, Burkina Faso da Nijar na kulla kawance mai karfi da ‘yanci, bayan ficewarsu daga ECOWAS da suak zarga da zama ‘yar amshin shatan kaashen yamma musamman faransa wacce ta yi musu mulin mallaka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ziyararsa A Birtaniya Da Ireland Da Halartar Taron Kolin Kwamitin Sulhu Da Na Tsaro A Munich Da Na G20
A jiya Asabar 22 ga wannan wata, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya yi bayani ga kafofin watsa labaru na kasar Sin bayan da ya kammala ziyararsa a Birtaniya da Ireland, da halartar taron kiyaye tsaro na Munich karo na 61, da shugabantar taron kolin kwamitin sulhun MDD a birnin New York, da kuma halartar taron ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar G20 a kasar Afirka ta Kudu.
A matsayin kasar da take shugabantar kwamitin sulhun MDD a wannan wata, kasar Sin ta yi kira ga taron koli na kwamitin mai taken “Bin ra’ayin bangarori daban daban da yin kwaskwarima kan kyautata aiwatar da harkokin duniya”. Inda game da hakan, Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin ta yi bayani game da ra’ayinta na kafa tsarin daidaita harkokin duniya cikin adalci, wato tabbatar da zaman daidaito kan ikon mallakar kasa, da tabbatar da adalci da yin hadin gwiwa da kuma bin taswirar aiwatar da ayyuka, kuma ra’ayin na kasar Sin ya samu amincewar kasashen da suka halarci taron.
Game da kara kaimin samar da yanayin dogaro da bangarori masu yawa maimakon daya tilo, Wang Yi ya yi nuni da cewa, yin hakan a duniya shi ne muhimmin ra’ayi da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, kuma shi ne kyakkyawan fatan da kasar Sin ta nuna wa duniya. Kana, kasar Sin za ta tabbatar da tsarin dogaro da bangarori masu yawa, da samar da gudummawa ga duniya yayin da ake fuskantar sauyin duniya.
Ban da wannan kuma, Wang Yi ya bayyana cewa, za a gudanar da taron kolin shugabannin kasashen kungiyar G20 a watan Nuwamban bana a nahiyar Afirka a karo na farko. Wannan shi ne lokacin da nahiyar Afirka ta samu cikakkiyar dama a kungiyar G20 da kuma aiwatar da harkokin duniya, wanda ya shaida cewa, shi ne babban canji a tarihi ga yanayin tattalin arziki da siyasa na duniya, kuma lamarin yana da babbar ma’ana. A gun taron ministocin harkokin wajen kasashen kungiyar G20 a wannan karon a birnin Johannesburg dake Afirka ta Kudu kuwa, kasar Sin ta ce ya kamata a kara sauraron ra’ayin kasashen Afirka, da maida hankali ga batutuwan Afirka, da nuna goyon baya ga Afirka, da rike damar hadin gwiwa ta kungiyar G20 don sa kaimi ga samun ci gaba da wadata a nahiyar ta Afirka. Wannan ra’ayi ya samu amincewar kasa da kasa. (Zainab Zhang)