Kasashen Kawancen Sahel Sun Kadaddamar Da Tutar Kungiyar
Published: 25th, February 2025 GMT
Kasashen nan guda uku mambobin kungiyar kawancen Sahel (AES) da suka balle daga kungiyar ECOWAS, sun kaddamar da tutarsu ta bai daya.
An kadaddamar da tutar ne a yayin haduwar ministocin harkokin wajen kasashen jiya Asabar a Bamako babban birnin kasar Mali mai rike da shugabancin kungiyar na farko.
Firaministan Mali, Janar Abdoulaye Maïga ya bayyana a yayin bikin, cewa “Tutar kungiyar AES, launin kore, tana dauke da tambarin kungiyar a tsakiyarta.
Ya jaddada cewa launin kore yana nuna alamar bege da wadata, wanda ke wakiltar dukiya da karfin tattalin arziki.
Wannan sabuwar alamar ta kunshi hadin kai da muradin bai daya na kasashen uku, inda suka kuduri aniyar yin aiki tare domin bunkasa tattalin arziki da zamantakewar yankin inji shi.
Kaddamar da wannan tuta na zuwa ne kasa da wata guda bayan da aka kaddamar da fasfo din kungiyar a ranar 29 ga watan Janairun 2025, Da nufin karfafa hadin gwiwarsu da saukaka zirga-zirgar jama’a da kayayyaki cikin ‘yanci a cikin yankin.
Wannan taron, wanda wani bangare ne na taron ministocin da ke ci gaba da gudana har zuwa ranar 23 ga watan Fabrairu, ya tabbatar da aniyar Mali, Burkina Faso da Nijar na kulla kawance mai karfi da ‘yanci, bayan ficewarsu daga ECOWAS da suak zarga da zama ‘yar amshin shatan kaashen yamma musamman faransa wacce ta yi musu mulin mallaka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Tana Shirin Mikawa HKI Dubban Boma-Bomai Cikin Makonni Masu Zuwa
Gwamnatin Amurka ta amince da shirin mikawa HKI dubban boma-bomai saboda kashe falasdinawa a Gaza.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa, sojojin HKI suna jiran isowar boma-bomai daga kasar Amurka don fara wani aikin soje na musamman a Gaza. Saboda kawo karshen samuwar Falasdinawa a yankin.
Wata majiyar HKI, yahudawa ta fadawa kamfanin dillancin labaran ‘Ynetnews’ kan cewa sojojin sama na HKI su na dakon isowar boma-bomai har 3000 daga kasar Amurka a cikin yan makonni masu zuwa.
Labarin ya kara da cewa rundunar ta na son ta gudanar da ayyukan soje mai fadin gaske a kan Falasdinwa wanda ya zai kawo karshen Hamas ya kuma kawo karshen samuwar Falasdinawa a yankin.
Labarin ya kara da cewa gwamnatin kasar Amurka ta na shirin aiko da wani karin boma –bomai har 10,000 nan gaba. Yahuda zasu yi amfani da wadannan boma-boman don fadada ayyukansu a yankin, wadanda suka hada da Siriya da Lebanon da kuma ita Gaza.