HausaTv:
2025-04-17@08:19:06 GMT

Rasha : Putin Ya Ce Turawa ‘Na Iya Shiga’ A Sasanta Rikicin Ukraine

Published: 25th, February 2025 GMT

Shugaban kasar Rasha Vladmir Putin ya bayanna cewa, Turawa za su iya shiga cikin shirin warware rikicin Ukraine, yayin da kungiyar EU ke fargabar cewa za a mayar da ita saniyar ware tun bayan fara tattaunawar kai tsaye tsakanin Moscow da Washington.

“Turawa, amma har da sauran kasashe, suna da hakki kuma suna da damar shiga, Kuma zamu mutunta hakan, ”in ji Vladimir Putin a wata hira da aka yi da shi ta talabijin.

Ya nanata cewa kasashen Turai ne suka yanke alaka da Rasha bayan da ta fara kai hari kan Ukraine shekaru uku da suka gabata, Don haka “Shigowarsu a cikin tsarin tattaunawar ya zama dole.

Vladimir Putin ya dage kan cewa tattaunawar da Rasha da Amurka suka yi a makon jiya a Saudiyya, wadda ita ce ta farko a wannan matakin tun farkon rikicin, na da nufin karfafa kwarin guiwa tsakanin Moscow da Washington.

Kafin hakan dai Ministocin harkokin wajen Rasha da Amurka Sergei Lavrov da Marco Rubio sun tattauna a Saudiyya kan “matsalolin da ke da nasaba da rikicin na Ukraine, amma ba batun rikicin Ukraine din ba,” a cewar Vladimir Putin.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Lauyoyin London Suna Tattara Bayanai Kan ‘Yan Birtaniya Da Suka Yi  Yaki Cikin Sahun Yahudawan Sahayoniyya A Gaza

Lauyoyin Landan suna tattara bayanai kan ‘yan Birtaniya da suka yi aiki a cikin rundunar sojojin mamayar Isra’ila

Kwararru kan harkokin shari’a na kasar Biritaniya sun ce gurfanar da wasu ‘yan kasar masu takardar ‘yan kasa biyu da ke aiki a cikin sojojin mamayar Isra’ila a gaban kuliya bisa zargin hannu a tafka laifukan yaki a Gaza, zai yi tasiri ga wadanda ke tunanin shiga cikin sahunsu.

Hakan ya biyo bayan gabatar da rahoto ga rundunar ‘yan sandan birnin Landan ne mai kunshe da shaidun da suka shafi ‘yan Birtaniya guda 10 da suka yi aikin soja karkashin rundunar mamayar haramtacciyar kasar Isra’ila da ake zargi da aikata laifukan yaki a Gaza.

A cewar wani rahoto da kamfanin dillancin labarai na Anadolu ya wallafa, lauyoyin cibiyar kare hakkin jama’a da cibiyar kare hakkin bil’adama ta Falasdinu sun gabatar da rahoto ga sashin yaki da ta’addanci na ‘yan sandan birnin London, wanda kuma ke binciken laifukan yaki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar sun sasanta
  • Najeriya da gwamnatin sojin Nijar da Nijar sun sasanta
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 157, Sun Ƙwato Bindigu Da Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • An Kashe Mutane 7 A Yayin Da ‘Yan Ta’adda Suka Ƙaddamar Da Wani Sabon Hari A Adamawa
  • Rasha ta ce tana bibiyar tattaunawar Iran da Amurka matuka
  • ‘Yan Ta’adda Sun Tarwasta Gadar Mandafuma A Jihar Borno
  • Hamas Ta Fadawa Iyalan Yahudawan Da Take Tsare Dasu A Gaza Kan Cewa ‘Ya’yansu Zasu Koma A Cikin Akwatunan Gawaki
  • Samarwa Matasa Abun Yi Shi Zai Kawo Ƙarshen Ta’addancin Boko Haram Da ‘Yan Bindiga – Zulum 
  • Lauyoyin London Suna Tattara Bayanai Kan ‘Yan Birtaniya Da Suka Yi  Yaki Cikin Sahun Yahudawan Sahayoniyya A Gaza
  • Rasha Ta Sanar Da Kashe Manyan Kwamandojin Sojin Ukraine Fiye Da 60 A Birnin Sumy Na Kasar Ta Ukraine