HausaTv:
2025-02-25@10:26:50 GMT
Amurka Ta Laftawa Iran Wasu Sabbin Takunkumai
Published: 25th, February 2025 GMT
Gwamnatin Trump ta saka sabbin takunkumai kan wasu mutane da ke da alaka da wani kamfanin fitar da mai na Iran.
Takunkuman sun shafi mutane 22 da jiragen ruwa 13 da ke da alaka da masana’antar mai ta Iran.
Wadannan takunkumin wani bangare ne na matsin lamba na shugaban Amurka Donald Trump kan Iran.
Ma’aikatar Baitulmali ta Amurka ta sanar da cewa, takunkumin na da nufin gurgunta harkokin hada-hadar kudi da kuma cinikin man fetur na Iran, da nufin takaita shirinta na nukiliya.
Iran dai na mai kakkausar suka kan takunkuman na Amurka, tana mai kallonsu a matsayin sabawa ka’idojin kasa da kasa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন: