Araghchi : Bai Kamata A Rika Murgude Hakkin Dan Adam Ana Shishigi A Harkokin Cikin Gidan Kasashe Ba
Published: 25th, February 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran, ya bayyana cewa bai kamata a yi amfani da hakkin dan adam a matsayin abun matsin lamba na siyasa ko tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kasashe ba.
Abbas Araghchi, ya bayyana hakan ne a zaman kwamitin kare hakkin bil adama na Majalisar Dinkin Duniya, inda ya jaddada cewa, daya daga cikin manyan abubuwan da ke kawo cikas ga tabbatar da hakkin dan Adam a duniya shi ne amfani da matakan tilastawa kasashe.
Ya kara da cewa wadannan matakan suna da illa ga fararen hula kuma ba adalci ne ba ga marasa galihu kamar mata, yara, tsofaffi da masu nakasa.
Ministan harkokin wajen kasar Iran Seyyed Abbas Araghchi ya bayyana jin dadinsa a wannan zama inda Ya ce: Jamhuriyar Musulunci ta Iran a matsayinta na daya daga cikin kasashen da suka assasa Majalisar Dinkin Duniya, a ko da yaushe tana mutunta daidaito da adalci a matakin koli. »
Araghchi ya bayyana cewa shekaru da dama da suka gabata al’ummar Iran na fuskantar manyan kalubale kamar takunkumin karya tattalin arziki da kuma ta’addanci, wadanda suka yi illa ga hakkokinsu na zamantakewa da tattalin arziki, To sai dai kuma a cewarsa duk da wadannan kalubale, Iran ta samu ci gaba mai ma’ana A tsarin Musulunci da mutuncin bil’adama, da inganta fannonin ilimi da kiwon lafiya da ‘yancin mata da ci gaban masana’antu da tattalin arziki.
Muna bukatar a gaggauta soke duk wani takunkumi, saboda ba wai kawai take hakkin bil’adama na al’ummar Iran ba ne, har ma da haifar da wahala ga miliyoyin mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista
Ministan Wutar Lantarki, Adedayo Adelabu ya bayyana cewa kimanin ’yan Najeriya miliyan 150 ne yanzu ke samun isasshiyar wutar lantarki, yayin da miliyan 80 ke da ƙarancin wutar lantarki.
Ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis a yayin taron sabunta sassan ministoci na 2025 da aka gudanar a Abuja, inda ya yi magana tare da ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Malagi, da sauran masu ruwa da tsaki.
ISWAP sun ruguza gadar Mandafuma a Borno ’Yan bindiga sun sace makiyaya 5, da shanu 1,200 a KadunaAdelabu ya bayyana cewa ci gaban ya samo asali ne daga shigar Najeriya cikin shirin “Mission 300” – wani gagarumin ƙoƙarin haɗin gwiwa na Bankin Duniya da Bankin Raya Afirka (AfDB) da nufin samar da wutar lantarki ga ‘yan Afirka miliyan 300 nan da shekarar 2030.
“Ƙa’idar ta tsara kyawawan manufofi don haɓaka hanyoyin samar da wutar lantarki, ƙara haɓaka makamashi da inganta hanyoyin magance matsalolin dafa abinci mai tsabta ga miliyoyin ‘yan Najeriya – wato Mission 300, kuma muna samun ci gaba mai kyau a kan wannan,” in ji shi.
Ya ci gaba da cewa, “Ina mai farin cikin gaya muku cewa cikin ‘yan Afirka miliyan 300 da Bankin Duniya da AfDB ke son cimmawa, Najeriya na kan hanyar da za ta biya ƙasa da kashi 25 cikin 100, wanda ke nufin kusan ‘yan Najeriya miliyan 75. Da muka gabatar da yarjejeniyarmu, sun amince da mu.”