Ba Ni Da Sha’awar Takarar Shugaban Ƙasa A 2031 – Nuhu Ribadu
Published: 25th, February 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.এছাড়াও পড়ুন:
Masu Kira ta Waya a Shirin FRCN Kaduna Sun Koka Kan Jinkirin Biyan Fansho
Masu kira ta waya a shirin Zamani Abokin Tafiya na FRCN Kaduna sun bayyana damuwa kan jinkirin biyan basussukan fansho ga tsofaffin ma’aikata duk da umarnin shugaban ƙasa da aka bayar kwanan nan.
Sun jaddada bukatar jami’an da ke kula da lamarin su hanzarta aiwatar da biyan kuɗaɗen domin girmama sadaukarwar da dattawan ƙasa suka yi da kuma rage cin hanci da rashawa a hidimar jama’a.
Masu kiran sun yi kira ga jami’ai da su nuna kishin ƙasa da tsoron Allah a yayin gudanar da aikinsu domin cika burin al’umma da kuma ci gaban ƙasa.
Alhaji Ibrahim Muhammad Katsina, Isya Soba, Ibrahim Allarama, Umar Aliyu Soba, Shafi’u Nalantawa, da Maza Jiya Soba, waɗanda su ma suka yi kira, sun jaddada bukatar inganta tsaro da rage farashin kayan masarufi bisa ga alkawarin da Gwamnatin Tarayya ta dauka.
SULEIMAN KAURA