Aminiya:
2025-04-17@02:37:04 GMT

Magidanci ya sari matarsa da adda har lahira

Published: 25th, February 2025 GMT

’Yan sanda sun cika hannu da wani magidanci bayan da ya sari matarsa da adda a kai, ta ce ga garinku nan.

’Yan sanda sun kama magidancin ne bayan samun rahoton aika-aikan da ya yi wa mai dakin tasa a sakamakon takaddamar da suka samu a tsakaninsu.

Lamarin ya faru ne a sabuwar unguwar Upper Mission da ke garin Benin, hedikwatar Jihar Edo.

Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Moses Yamu, ya ce ko da ’yan sanda daga babban ofishinsu da ke yankin Aduwawa suka isa wurin, sun iske matar kwance cikin jini, da mummunan sara a kanta.

Ya daɓa wa yayansa wuƙa saboda Naira 700 NAJERIYA A YAU: Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi? Luwaɗi: An yanke wa ɗalibai biyu hukuncin bulala a bainar jama’a

Ya ce, al’ummar yankin sun nemi su halaka shi saboda saran matar tasa da ya yi da makami, amma ya sha da kyar.

Ya bayyana cewa da kyar ’yan sanda suka kwaci mutumin daga hannun jama’a, suka tafi da shi domin tsarewa da kuma yi masa tambayoyi.

CSP Moses Yamu ya ce ’yan sanda sun kai matar asibiti inda likita ya shaida musu cewa rai ya riga ya yi halinsa.

Jami’in ya kara da cewa Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Edo, Betty Otimenyin, ya koka bisa yadda ake samu karuwar fada da makami a tsakanin ma’aurata a jihar.

Daga nan ya ba da umarnin a gudanar da zuzzurfan bincike kan lamarin domin hukunta mai laifi yadda doka ta tanadar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Matarsa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Ta’adda Sun Tarwasta Gadar Mandafuma A Jihar Borno

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutane 7 A Yayin Da ‘Yan Ta’adda Suka Ƙaddamar Da Wani Sabon Hari A Adamawa
  • ‘Yan Ta’adda Sun Tarwasta Gadar Mandafuma A Jihar Borno
  • Matashi ya kai kansa ofishin ’yan sanda
  • Yadiot Ahranot: Amurka Ta Bayyana Lokacin Ficewarta Daga Syria
  • Dalilin da Kwankwaso zai dawo APC — Ganduje
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan (a) 109
  • An yi garkuwa da masu ibada a Kogi
  • Sojoji sun kama ’yan bindiga 12 a Nijar
  • Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda