Aminiya:
2025-02-25@12:54:40 GMT

Magidanci ya sari matarsa da adda har lahira

Published: 25th, February 2025 GMT

’Yan sanda sun cika hannu da wani magidanci bayan da ya sari matarsa da adda a kai, ta ce ga garinku nan.

’Yan sanda sun kama magidancin ne bayan samun rahoton aika-aikan da ya yi wa mai dakin tasa a sakamakon takaddamar da suka samu a tsakaninsu.

Lamarin ya faru ne a sabuwar unguwar Upper Mission da ke garin Benin, hedikwatar Jihar Edo.

Kakakin ’yan sandan jihar, CSP Moses Yamu, ya ce ko da ’yan sanda daga babban ofishinsu da ke yankin Aduwawa suka isa wurin, sun iske matar kwance cikin jini, da mummunan sara a kanta.

Ya daɓa wa yayansa wuƙa saboda Naira 700 NAJERIYA A YAU: Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi? Luwaɗi: An yanke wa ɗalibai biyu hukuncin bulala a bainar jama’a

Ya ce, al’ummar yankin sun nemi su halaka shi saboda saran matar tasa da ya yi da makami, amma ya sha da kyar.

Ya bayyana cewa da kyar ’yan sanda suka kwaci mutumin daga hannun jama’a, suka tafi da shi domin tsarewa da kuma yi masa tambayoyi.

CSP Moses Yamu ya ce ’yan sanda sun kai matar asibiti inda likita ya shaida musu cewa rai ya riga ya yi halinsa.

Jami’in ya kara da cewa Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar Edo, Betty Otimenyin, ya koka bisa yadda ake samu karuwar fada da makami a tsakanin ma’aurata a jihar.

Daga nan ya ba da umarnin a gudanar da zuzzurfan bincike kan lamarin domin hukunta mai laifi yadda doka ta tanadar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Matarsa

এছাড়াও পড়ুন:

An Bukaci Kafa Dokar Hukuncin Kisa Ga Masu Safarar Da Shan Miyagun Kwayoyi

 

An bukaci Majalisar Dokoki ta Kasa da ta kafa doka wacce za ta tanadi hukuncin kisa ga masu safarar da kuma masu shan miyagun kwayoyi, domin kare rayuwar ‘yan kasa.

Wannan kiran ya fito ne daga shirin KAKAKI na FRCN Kaduna FM, inda masu kira suka bayyana ra’ayoyinsu a yayin tattaunawa da mai gabatar da shirin.

Masu magana sun nuna damuwa kan illar safarar miyagun kwayoyi a kasar, musamman yadda yake shafar matasa, wadanda ake kallon su a matsayin shugabannin gobe.

Alhaji Gaddafi Rigasa da Hajiya Aisha Mando sun jaddada bukatar hukumomin tsaro su kara zage damtse wajen yaki da wannan matsala, domin inganta ci gaban tattalin arziki da zamantakewa.

Sai dai sun kuma ba da shawarar a farfado da masana’antu a yankin Arewa a matsayin hanya daya daga cikin hanyoyin rage rashin aikin yi, wanda ke haddasa lalacewar matasa da kuma tabarbarewar tsaro.

SULEIMAN KAURA

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bukaci Kafa Dokar Hukuncin Kisa Ga Masu Safarar Da Shan Miyagun Kwayoyi
  • Gwamnatin Iraki Ta Kokawa Sabuwar Gwamnatin Siriya Dangane Da Barazanar Mayakan Daesh Da Suka Rage A Kasar
  • Matar aure ta banka wa mijinta wuta
  • Yadda jama’a suka kama ɗan shekara 65 ɗauke da bindiga
  • An kama mutum biyu kan kisan wata mata saboda maita
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Wani Mutum Tare Da Sace Mutum Biyu A Kaduna
  • PDP ta lashe zaɓen ƙananan hukumomin Osun
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Alhassan (a) 20
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Alhassan (a) 19