Aminiya:
2025-04-17@03:39:37 GMT

Luwadi: Magijanci ya lalata dan shekara 5 a Zariya

Published: 25th, February 2025 GMT

Mutanen unguwa sun kama wani magidanci mai shekara 45 kan zargin sa da lalata wani yaro ɗan makarantar firamare ta hanyar luwadi a yankin Zariya ta Jihar Kaduna.

Al’ummar yankin sun ce dama ana zargin mutumin da yi wa yara maza fyade, don haka suke ta bibiyar motsinsa, kuma yaron ya faɗa da bakinsa cewa kusan sau uku mutmin yana ɗaukar sa.

Wanda ke zargin yana sana’ar sayar da rake ne a Bakin Dago Tudun Jukun a Karamar Hukumar Zariya Jihar Kaduna.

Aminiya ta ziyarci xibiyar da ke kula da cin zarafin mata da ƙananan yara da ke Asibitin Gambo Sawaba Kofar Gayan Zariya domin samun sahihin bayani kan lamarin a likitance.

Magidanci ya sari matarsa da adda har lahira Ya daɓa wa yayansa wuƙa saboda Naira 700 Luwaɗi: An yanke wa ɗalibai biyu hukuncin bulala a bainar jama’a

Manajar Cibiyar, Hajiya A’isha Ahmed ta ce a ranar 12 ga watan 2 2025 ofishin ’yan sanda da ke Gonar Ganye, gundumar Tukur Tukur ya kawo wani yaro ɗan shekara 5 kuma ɗan aji ɗaya a makarantar firamare da ake zargin mutumin da lalatawa.

Bayan likitoci sun duba sun gano cewa yaron duburarsa ta bude, wanda hakan ke nuni da an yi yunƙurin zakke masa ta duburarsa.

Hajiya A’isha Ahmed ta ce sun dora yaron a kan magani har na tsawon kwanaki 28 kuma za su rika bibiyar sa domin su tabbatar da cewa yana amfani da maganin yadda ya kamata.

Ta ci gaba da cewa za ta tura sakamakon zuwa ga Kwamishinan Lafiya na Jihar Kaduna, kuma ta tabbatar da cewa sun bai wa jami’an ’yan  sanda kwafin binciken.

Hajiya A’isha Ahmed ta yi kira ga iyaye da su daina boye irin wannan mugun abin da ke faruwa da yaransu wai don gudun abin kunya ko halin da yaran za su shiga.

Ta kara da cewa zuwa asibitin da yaran da aka ci zarafinsu a kan lokaci yana taimakawa wajen kula da lafiyarsu.

Mahaifin yaron da aka ɓata ya koka kan yadda ya ce wasu makusantan wanda ake zargin suke ƙoƙarin ɗanne shi da kuma kare shi wanda ake zargin.

Ya ce “abin mamaki shi ne ta yadda suka bi ta hannun mai anguwa wai a bani kuɗi na bar maganar,” DOn haka ya ce a shirye yake da ya bi haƙƙin ɗan nasa domin daƙile irin hakan a nan gaba ga ’ya’yan wasu.

Duk ƙoƙarin jin ta bakin mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ASP Mansur Hassan, ya ci tura, domin layin wayarsa ta ƙi shiga, kuma har rubutaccen sakon da aka aika masa bai amsa ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Luwadi yaro Jihar Kaduna

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC ta gaza tabbatar da tuhumar Murja kan zargin wulaƙanta takardar Naira

Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arzikin Nijeriya ta’annati, ta gaza tabbatar da zargin wulaƙanta takardar Naira da take yi wa fitacciyar ’yar TikTok ɗin nan, Murja Ibrahim Kunya.

A bayan nan ne EFCC ta gurfanar da Murja a gaban kotu kan zargin cewa ta ci karo da wani bidiyonta tana rawa a kan takardun kuɗi har kimanin Naira dubu 400.

A ƙunshin ƙarar da EFCC ta gabatar mai lamba FHC/KN/CS/18/2025 a gaban wata Kotun Tarayya da ke zamanta a Kano, ta ce laifin da take tuhumar Murja tanadi na Kundin Dokokin Babban Bankin Nijeriya CBN wanda ya haramta wulaƙanta takardar Naira ta kowace siga.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hisbah ta kama matashi yana ‘baɗala’ da Akuya a Kano
  • Dalilin da Kwankwaso zai dawo APC — Ganduje
  • Majalisar Kaduna ta Amince da Kudirin Kula da Lafiyar Kwakwalwa na Jihar
  • EFCC ta gaza tabbatar da tuhumar Murja kan zargin wulaƙanta takardar Naira
  • Matashi ya yi yunƙurin soka wa mahaifinsa makami a Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • ’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta
  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna