Luwadi: Magijanci ya lalata dan shekara 5 a Zariya
Published: 25th, February 2025 GMT
Mutanen unguwa sun kama wani magidanci mai shekara 45 kan zargin sa da lalata wani yaro ɗan makarantar firamare ta hanyar luwadi a yankin Zariya ta Jihar Kaduna.
Al’ummar yankin sun ce dama ana zargin mutumin da yi wa yara maza fyade, don haka suke ta bibiyar motsinsa, kuma yaron ya faɗa da bakinsa cewa kusan sau uku mutmin yana ɗaukar sa.
Wanda ke zargin yana sana’ar sayar da rake ne a Bakin Dago Tudun Jukun a Karamar Hukumar Zariya Jihar Kaduna.
Aminiya ta ziyarci xibiyar da ke kula da cin zarafin mata da ƙananan yara da ke Asibitin Gambo Sawaba Kofar Gayan Zariya domin samun sahihin bayani kan lamarin a likitance.
Magidanci ya sari matarsa da adda har lahira Ya daɓa wa yayansa wuƙa saboda Naira 700 Luwaɗi: An yanke wa ɗalibai biyu hukuncin bulala a bainar jama’aManajar Cibiyar, Hajiya A’isha Ahmed ta ce a ranar 12 ga watan 2 2025 ofishin ’yan sanda da ke Gonar Ganye, gundumar Tukur Tukur ya kawo wani yaro ɗan shekara 5 kuma ɗan aji ɗaya a makarantar firamare da ake zargin mutumin da lalatawa.
Bayan likitoci sun duba sun gano cewa yaron duburarsa ta bude, wanda hakan ke nuni da an yi yunƙurin zakke masa ta duburarsa.
Hajiya A’isha Ahmed ta ce sun dora yaron a kan magani har na tsawon kwanaki 28 kuma za su rika bibiyar sa domin su tabbatar da cewa yana amfani da maganin yadda ya kamata.
Ta ci gaba da cewa za ta tura sakamakon zuwa ga Kwamishinan Lafiya na Jihar Kaduna, kuma ta tabbatar da cewa sun bai wa jami’an ’yan sanda kwafin binciken.
Hajiya A’isha Ahmed ta yi kira ga iyaye da su daina boye irin wannan mugun abin da ke faruwa da yaransu wai don gudun abin kunya ko halin da yaran za su shiga.
Ta kara da cewa zuwa asibitin da yaran da aka ci zarafinsu a kan lokaci yana taimakawa wajen kula da lafiyarsu.
Mahaifin yaron da aka ɓata ya koka kan yadda ya ce wasu makusantan wanda ake zargin suke ƙoƙarin ɗanne shi da kuma kare shi wanda ake zargin.
Ya ce “abin mamaki shi ne ta yadda suka bi ta hannun mai anguwa wai a bani kuɗi na bar maganar,” DOn haka ya ce a shirye yake da ya bi haƙƙin ɗan nasa domin daƙile irin hakan a nan gaba ga ’ya’yan wasu.
Duk ƙoƙarin jin ta bakin mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ASP Mansur Hassan, ya ci tura, domin layin wayarsa ta ƙi shiga, kuma har rubutaccen sakon da aka aika masa bai amsa ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda Luwadi yaro Jihar Kaduna
এছাড়াও পড়ুন:
Zamu Tabbatar Ingantuwar Depon Sojoji Na Zaria – Ministan Tsaro Badaru
Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar ya yi alkawarin inganta sansanin horas da kuratan sojoji dake Zaria wato Depot domin baiwa hukumar Soji damar ci gaba da aikin horaswa a wajen.
Ministan ya yi wannan alkawarin ne a lokacin da ya kai ziyarar tantance sojojin Najeriya da ke Chindit Cantonment a Zariya.
Ministan ya kuma ce, ma’aikatar tsaro ba za ta bar wani abu ba, wajen tabbatar da cewa makarantar firamare ta Chindit ta samu ingantuwar kayan aiki don dacewa da tsarin zamani a matsayin hanyar kara kwarin gwiwa na hafsoshi da sojoji na Kantoment da ke amfana da wajen.
Ya kara da cewa ofishin sa zai hada kai da gwamnatin jihar Kaduna domin ganin an kammala makarantar sakandare ta Chindit.
Ministan ya kuma yi alkawarin taimakawa wajen hakar wasu rijiyoyin burtsatse masu amfani da hasken rana domin kara inganta rijiyoyin burtsatse da ke cikin Depot din domin rage kalubalen da ke tattare da samar da ruwan sha a yankin.
Da yake jawabi tun da farko, kwamandan, Depot, Manjo Janar Ahmed Mohammed ya gode wa ministan bisa wannan ziyara, sannan ya kuma sanar da shi yadda babban hafsan sojin kasa, Laftanar-Janar Olufemi Oluyede ya yi don magance kalubalen da ke fuskantar Depot din.
Ya kuma bayyana fatan cewa wannan hadin gwiwa zai sanya Depot a kan hanyar da ta dace don ganin ta cika aikinta na samarda sojojin Nijeriya.
Kwamandan ya bada tabbacin cewa za a kula da jin dadin ma’aikata da wadanda aka dauka yadda ya kamata domin tabbatar da cewa hukumar ta samu cikakkiyar damar cimma muradun Najeriya.
REL/HALIRU HAMZA