HausaTv:
2025-03-28@06:44:15 GMT

Mutum 7,000 Suka Mutu A Rikicin Gabashin Kwango Tun Daga Watan Janairu

Published: 25th, February 2025 GMT

Fiye da mutane 7,000 da yawancinsu fararen hula ne aka kashe a yankin gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango tun daga watan Janairu, in ji Firaminista Judith Suminwa Tuluka a ranar Litinin.

Mambobin kungiyar M23 da ke samun goyon bayan kasar Rwanda sun kwace iko da yankunan gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kongo masu arzikin ma’adinai da suka hada da manyan biranen Goma da Bukavu da ke gabashin kasar.

Firayim Minista Judith Suminwa Tuluka ta yi gargadin cewa, halin da ake ciki na tsaro a gabashin DRC ya kai matsayi mai daukar hankali, yayin da take jawabi ga kwamitin kare hakkin bil’adama na Majalisar Dinkin Duniya a Geneva.

Ta ce mutanen da suka mutu sun hada da “fiye da gawarwaki 2,500 da aka binne ba a san ko su waye ba” kuma gawarwakin mutane 1,500 na nan a dakin ajiye gawa.

A cewar rahotannin Majalisar Dinkin Duniya, ‘yan kungiyar M23 dauke da makamai, wadanda ke samun goyon bayan sojojin Rwanda kimanin 4,000, suyka abkawa yankunan, lamarin da ya tilastawa dubban mutane tserewa daga yankin.

A baya-bayan nan ne dakarun M23 suka karbe iko da Bukavu, babban birnin lardin Kivu ta Kudu, bayan da suka kwace Goma, babban birnin lardin Kivu ta Arewa.

Firayim Ministan Kongo ya ce an kashe fiye da mutane 3,000 a Goma kadai.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Sayi Man Jiragen Sama Fiye Da Ganga Miliyan 2 Daga Matatar Dangote A Watan Maris

Amurka ta shigo da sama da ganga miliyan biyu na man jiragen sama daga matatar Dangote a watan Maris.

Matatar ta tabbatar da hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, inda ta ce hakan ya tabbatar da “nagartar da ba ta misaltuwa” na kayayyakin matatar da kuma aminci da kasashen duniya suka bai wa matatar.

Duba daga  rahoton ma’aikatar sa ido kan zirga-zirgar jiragen ruwa ta Kpler, ta ce jiragen ruwa shida dauke da kusan ganga miliyan 1.7 na man jiragen sama daga matatar Dangote sun isa tashoshin jiragen ruwa na Amurka a wannan watan na Maris.

Wani jirgin ruwa, Hafnia Andromeda, ana kyautata tsammanin zai isa tashar Everglades a ranar 29 ga Maris tare da kusan ganga 348,000 na man jirgin sama daga matatar Dangote.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Halin Da Matasa Suka Tsinci Kansu A Najeriya
  • Duniyarmu A Yau: Ranar Qudus Ta Duniya Ta Shekara 1446
  • Mutum 2 sun rasu, wani ya ji rauni a hatsarin mota a Kano
  • ’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa
  • Wani Bawan Allah Ya Rasu Jim Kadan Bayan Sallar Asuba A Wani Masallaci A Abuja
  • Gobarar daji ta kashe mutum 24 a Koriya ta Kudu
  • Rikicin Masarauta: Duk mai ja da hukuncin Allah ba zai yi nasara ba — Sanusi II
  • Amurka Ta Sayi Man Jiragen Sama Fiye Da Ganga Miliyan 2 Daga Matatar Dangote A Watan Maris
  • NIDCOM: An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Kurkuku A Libya
  • NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi