HausaTv:
2025-03-28@04:56:09 GMT

Iran : Makaman Kare Dangi Na Israila Barazana Ne Ga Zaman Lafiya Da Tsaro

Published: 25th, February 2025 GMT

Iran ta bakin Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ta shaidawa taron kwance damarar makamai na Majalisar Dinkin Duniya a Geneva cewa, makaman kare dangi na gwamnatin Isra’ila da suka hada da makaman nukiliya na ci gaba da yin barazana ga zaman lafiya da tsaro a yankin da ma duniya baki daya.

A yayin jawabin da ya yi a ranar Litinin, a babban taro na 2025 kan kwance damara, a hedkwatar MDD dake Geneva, Mr.

Araghchi ya yi kira ga kasashen duniya da MDD da su ba da fifiko kan batun kawar da makaman nukiliya.

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa “dole ne kasashen duniya su tilastawa Isra’ila bin yarjejeniyar hana yaduwar makaman kare dangi (NPT) don kawar da dukkanin ayyukanta na nukiliya na kasa da kasa.

A yayin da yake bayyana damuwarsa kan barazanar makaman nukiliya da kuma mummunar illar da suke yi ga bil’adama da muhalli, Mr. Araghchi ya yi kira da a sanya makaman nukiliya a kan gaba wajen damuwar kasashen duniya da MDD.

Araghchi ya bayyana irin ayyukan da ba a taba ganin irinsa ba, da suka hada da kisan kare dangi, laifuffukan yaki da laifukan cin zarafin bil Adama da gwamnatin Isra’ila ta aikata a zirin Gaza, wanda ya yi sanadin lalata yankunan da aka yi wa kawanya tare da mutuwar dubban mutane, musamman mata, yara da kuma tsofaffi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: makaman nukiliya

এছাড়াও পড়ুন:

Aminu Ado ya soke hawan salla don gudun rikici a Kano

Sarkin Kano 15, Aminu Ado Bayero, ya soke shirinsa na gudanar da bikin hawan salla bayan shawarwari da dattawa da malaman addini suka ba shi.

Ya bayyana cewa matakin ya biyo bayan buƙatar tabbatar da zaman lafiya a jihar, biyo bayan shiga ruɗani da jama’a suka yi.

Hadimin Gwamnan Kano Tanka Galadanci ya rasu Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4

Wannan na zuwa ne yayin da aka shiga ruɗani a Kano saboda rikicin masarauta, biyo bayan mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano.

Tun farko, duka sarakunan biyu – Sanusi II da Aminu Ado Bayero, sun shirya gudanar da hawan salla, lamarin da ya haddasa fargaba a tsakanin al’umma.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a daren Laraba, Sarki Aminu, ya ce ya ɗauki matakin ne bayan jin ra’ayin malamai da dattawa.

“Malamai da dattawa sun shawarce mu, kuma muna mutunta su. Don haka, bayan nazari tare da majalisar masarauta, mun yanke shawarar cewa mun janye domin zaman lafiya,” in ji shi.

Idan za a tuna, a makon da ya gabata ne, Aminu Ado, ya aike wa ’yan sanda takardar neman izinin gudanar da hawan salla, bayan da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya umarci Muhammadu Sanusi II, ya shirya yin hawan salla a bana.

Sarkin ya jaddada cewa bikin hawan salla ba abu ne da ya zama wajibi ba idan zai iya haddasa rikici da asarar rayuka.

“Idan akwai fargabar cewa hawan salla zai haddasa tashin hankali da asarar rayuka ko dukiyoyi, to, yana da kyau a daina,” in ji shi.

A gefe guda, al’ummar Kano sun nuna damuwa kan yadda rikicin masarautar ke ci gaba da yin tasiri a rayuwarsu.

Ana sa ran wannan matakin zai rage fargabar da ake ciki, tare da tabbatar da zaman lafiya a Jihar Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aminu Bayero ya soke hawan Sallah
  • Sallah: ’Yansanda Sun Yi Alƙawarin Tabbatar Da Tsaro A Kano
  • Ranar Quds : Hamas ta bukaci masu huduba su sadaukar da jawabansu kan Falastinu
  • Aminu Ado Ya Soke Hawan Sallah Don Tabbatar Da Zaman Lafiya A Kano
  • Aminu Ado ya soke hawan salla don gudun rikici a Kano
  • Sin Za Ta Dauki Matakai Don Kiyaye Hakki Da Muradun Kamfanoninta
  • Hukumar IAEA ta yi ishara da yiwuwar sake komawa teburin tattaunawa tare da Iran
  • Araqchi: Har yanzu Iran ba ta mayar da amsa ga wasikar Trump kan tattaunawar nukiliya ba
  • Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Zargin Kasar Amurkan Dangane Da Kamfanonin Man Fetur Na Kasar Ba Gaskiya Bane