HausaTv:
2025-04-17@08:26:13 GMT

Iran : Makaman Kare Dangi Na Israila Barazana Ne Ga Zaman Lafiya Da Tsaro

Published: 25th, February 2025 GMT

Iran ta bakin Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ta shaidawa taron kwance damarar makamai na Majalisar Dinkin Duniya a Geneva cewa, makaman kare dangi na gwamnatin Isra’ila da suka hada da makaman nukiliya na ci gaba da yin barazana ga zaman lafiya da tsaro a yankin da ma duniya baki daya.

A yayin jawabin da ya yi a ranar Litinin, a babban taro na 2025 kan kwance damara, a hedkwatar MDD dake Geneva, Mr.

Araghchi ya yi kira ga kasashen duniya da MDD da su ba da fifiko kan batun kawar da makaman nukiliya.

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa “dole ne kasashen duniya su tilastawa Isra’ila bin yarjejeniyar hana yaduwar makaman kare dangi (NPT) don kawar da dukkanin ayyukanta na nukiliya na kasa da kasa.

A yayin da yake bayyana damuwarsa kan barazanar makaman nukiliya da kuma mummunar illar da suke yi ga bil’adama da muhalli, Mr. Araghchi ya yi kira da a sanya makaman nukiliya a kan gaba wajen damuwar kasashen duniya da MDD.

Araghchi ya bayyana irin ayyukan da ba a taba ganin irinsa ba, da suka hada da kisan kare dangi, laifuffukan yaki da laifukan cin zarafin bil Adama da gwamnatin Isra’ila ta aikata a zirin Gaza, wanda ya yi sanadin lalata yankunan da aka yi wa kawanya tare da mutuwar dubban mutane, musamman mata, yara da kuma tsofaffi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: makaman nukiliya

এছাড়াও পড়ুন:

Rasha ta ce tana bibiyar tattaunawar Iran da Amurka matuka

Rasha ta ce tana ta na sa ido sosai game da tattaunawa karo na biyu tsakanin Amurka da Iran kuma a shirye take ta taimaka wajen warware shirin nukiliyar Iran ta hanyar siyasa da diflomasiyya.

Makomar shirin nukiliyar Iran da kuma zaman lafiyar yankin na iya danganta ne kan ko Washington da Tehran za su koma kan teburin shawarwari.

Yayin da tattaunawar tsakanin Amurka da Iran ta tsaya cik a baya, manyan kasashen duniya musamman Rasha da China sun yi yunkurin ganin neman farfado da tattaunawar ta diflomasiyya.

Tunda farko a makon da ya gabata Majalisar Tarayyar Rasha ta amince da yarjejeniyar hadin gwiwa ta tsawon shekaru 20 a hukumance da Iran, wanda ke karfafa kawancen dogon lokaci tsakanin kasashen biyu a fannonin da suka hada da tsaro, makamashi da fasaha.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya sanar a yau Laraba cewa, zai je birnin Moscow domin kai  sakon Jagoran juyin juya halin musulinci Ayatollah Ali Khamenei ga shugaba Vladimir Putin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Yi Garambawul A Fannin Kiwon Lafiya
  • Araghchi: babu tattaunawa kan batun tace sinadarin uranium
  • Hamas ta bukaci hadin kan duniya domin kawo karshen kisan kiyashin da Isra’ila ke yi a Gaza
  • Rasha ta ce tana bibiyar tattaunawar Iran da Amurka matuka
  • Iran Ta Sanar Da Kasar Oman A Matsayin Wajen Tattaunawa Na Gaba Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Firaministan Malaysia: Xi Jinping Babban Jagora Ne Mai Matukar Mayar Da Hankali Kan Abubuwan Dake Shafar Zaman Rayuwar Jama’a
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Zanta Da Tokwaransa Na Kasar Kuwait
  • Shugaba Tinubu Ya Yi Allah-wadai Da Harin Jihar Filato
  • Kasashen Turai na E3 sun goyi bayan tattaunawar Iran da Amurka
  • Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran