An bukaci Majalisar Dokoki ta Kasa da ta kafa doka wacce za ta tanadi hukuncin kisa ga masu safarar da kuma masu shan miyagun kwayoyi, domin kare rayuwar ‘yan kasa.

Wannan kiran ya fito ne daga shirin KAKAKI na FRCN Kaduna FM, inda masu kira suka bayyana ra’ayoyinsu a yayin tattaunawa da mai gabatar da shirin.

Masu magana sun nuna damuwa kan illar safarar miyagun kwayoyi a kasar, musamman yadda yake shafar matasa, wadanda ake kallon su a matsayin shugabannin gobe.

Alhaji Gaddafi Rigasa da Hajiya Aisha Mando sun jaddada bukatar hukumomin tsaro su kara zage damtse wajen yaki da wannan matsala, domin inganta ci gaban tattalin arziki da zamantakewa.

Sai dai sun kuma ba da shawarar a farfado da masana’antu a yankin Arewa a matsayin hanya daya daga cikin hanyoyin rage rashin aikin yi, wanda ke haddasa lalacewar matasa da kuma tabarbarewar tsaro.

SULEIMAN KAURA

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwayoyi Safara

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin malami da azabtar da ɗalibi saboda shan mangwaro a makaranta

Ana zargin malamin makarantar Aliyu Mustapha Academy da ke Jimeta a Jihar Adamawa kan wuce gona da iri da kuma azabtar da wani ɗalibinsa a dalilin shan mangwaro a lokacin ‘break’ a harabar makarantar.

Aminiya ta ruwaito cewa a lokacin da ake tsaka da hutun tara ne malamin yan kama ɗalibin yana shan mangwaro, inda ya lakaɗa wa ɗalibin dukan tsiya.

Shaidu sun ce har da naushi malamin ya riƙa yi wa ɗalibin, lamarin da ya sa taron ya ƙuƙƙuje tare da barin sa da tabbai a jikinsa.

Malamin yana tsaka da dukan ɗalibin ne mahaifin yaron ya je makarantar domin tabbatar da biyan kudin makarantar ɗan nasa.

NAJERIYA A YAU: Matakan Kariya Daga Cutar Ƙyandar Biri Har yanzu Najeriya na buƙatar shugabanni nagari – Sheikh Gumi

Ganin halin da ya iske ɗan nasa a sai ya sanya baki, amma malamin bai dakata ba da naushin yaron.

Mahaifin mai suna Bashiru Haman, ya ce, “Na kaɗu da ganin ana dukan yaron haka, na yi ƙoƙarin in ƙwace shi amma malamin ya ƙi barin sa. Daga nan sai an kai ƙara wajen shugabar makarantar, Misis Amanda Pam, Amma sai ta umarce ni da in fice daga harabar makarantar.”

Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Adamawa, A’isha Yanar ta tabbatar da faruwar lamarin. Ta ce, “ma’aikatar ta samu wasikar ƙorafin mahaifin ɗalibin kuma ta fara gudanar da bincike domin daukar matakin da ya dace. Za kuma mu ɗauki matakan da suka kamata domin hana faruwar irin haka a nan gaba.”

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Adamawa ta ce ta fara gudanar da bincike kan lamarin, kamar yadda kakakinta, Dankombo Morris, ya sanar.

Ya ce, “muna kira da duk masu wani bayani game da abinda ya faru da su taimaka mana da bayanai a wannan bincike da muke gudanarwa.”

A halin yanzu dai yaron mai suna Jaafar yana fama da jinya a yayin da iyayensa suke neman a ƙwato masa haƙƙi kan azabtarwar da aka yi masa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 40% na matan Kano sun fuskaci cin zarafi a gida —Shugaban Majalisa
  • NAJERIYA A YAU: Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi?
  • Gwamna Namadi Ya Bukaci Wadanda Suka Amfana Da Tallafin Mazabu Su Zama Masu Dogaro Da Kai
  • Hajj 2025: NAHCON Ta Rage N54bn Daga Kudaden Cajin Maniyyata
  • Ana zargin malami da azabtar da ɗalibi saboda shan mangwaro a makaranta
  • Kungiyar RSF da kawayenta na shirin kafa gwamnatin ‘yan tawaye a Sudan
  • Hakuri Da Biyayya Su Ne Sirrin Ɗaukaka A Masana’antar Kannywood – Mu’azu
  • Masu Kira ta Waya a Shirin FRCN Kaduna Sun Koka Kan Jinkirin Biyan Fansho
  • Ƴansandan Katsina Sun Kwato Mutum 13 Daga Hannun Masu Garkuwa