Dan kwallon Najeriya ya mutu bayan fadowa daga bene a Uganda
Published: 25th, February 2025 GMT
Wani dan kwallon Najeriya mai suna Abubakar Lawal daga Jihar Sakkwato ya rasu bayan fadowa daga bane a kasar Uganda, inda yake taka leda.
Rahotanni sun bayyana cewa Abubakar Lawal mai shekaru 29 ya gamu da ajalinsa ne bayan ya fado daga hawa na uku na wanin babban kantin sayar da kayayyaki a Kampala, babban birnin kasar Uganda.
Rasuwar tasa ta haifar haifar da ce-ce-ku-ce a kasar, kamar yadda kafofin yada labarai suka ruwaito. Da farko an alakanta rasuwar tasa da hatsarin babur, kafin daga bisani jami’an tsaro su bayyana cewa ya fado ne daga bene.
Marigayin dan wasan gaba ne a kungiyar kwallon kafa ta Vipers da ke kasar, inda ya fara wasa tun shekara 2022, kafin nan ya shekara biyu yana taka lelda a kungiyar AS Kigali da ke kasar Rwanda.
Kungiyar Vipers ta sanar Abubakar ya rasu ne a ranar Litinin bayan da ya fado daga hawa na uku da kataferen kantin mai suna Voicemall Shopping Arcade a Kampala.
A sakon ta’aziyyarta, kungiyar ta bayyaan marigayin a matsayin, “mutumin kirki mai kyakkyawar zuciya, mai yawan kyauta ne da kuma taimaka wa jama’a,” kamar yadda ya wallafa a shafinta na X.
Runudar ’yan sandan ta sanar da fara bincike kan musabbabin mutuwar dan kwallon na Najeriya.
Hukumar ’yan sandan Uganda ta bayyana cewa dan wasan ya gamu da ajalinsa ne a lokain da ya kai wa wata kawarsa ’yar kasar Tanzaniya ziyara a rukunin ginin.
A sakon ta’aziyyar dan wasan, kungiyar Nasarawa United, tsohuwar kungiyar Abubakar, ta ce, “Muna jimaminin mutuwar fuju’ar tsohon dan wasanmu Abubakar Lawal, kuma muna rokon Allah Ya sada shi da rahama.”
Shi kuwa Mustafa Kizza, dan wasan Uganda, ya ce: “Rashin Lawal abu ne mai wuyar jurewa. Mutumin kirki ne mai fara da hazaka da ba za mu taba mantawa da shi ba.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Aminu Ado ya soke hawan salla don gudun rikici a Kano
Sarkin Kano 15, Aminu Ado Bayero, ya soke shirinsa na gudanar da bikin hawan salla bayan shawarwari da dattawa da malaman addini suka ba shi.
Ya bayyana cewa matakin ya biyo bayan buƙatar tabbatar da zaman lafiya a jihar, biyo bayan shiga ruɗani da jama’a suka yi.
Hadimin Gwamnan Kano Tanka Galadanci ya rasu Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4Wannan na zuwa ne yayin da aka shiga ruɗani a Kano saboda rikicin masarauta, biyo bayan mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano.
Tun farko, duka sarakunan biyu – Sanusi II da Aminu Ado Bayero, sun shirya gudanar da hawan salla, lamarin da ya haddasa fargaba a tsakanin al’umma.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a daren Laraba, Sarki Aminu, ya ce ya ɗauki matakin ne bayan jin ra’ayin malamai da dattawa.
“Malamai da dattawa sun shawarce mu, kuma muna mutunta su. Don haka, bayan nazari tare da majalisar masarauta, mun yanke shawarar cewa mun janye domin zaman lafiya,” in ji shi.
Idan za a tuna, a makon da ya gabata ne, Aminu Ado, ya aike wa ’yan sanda takardar neman izinin gudanar da hawan salla, bayan da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya umarci Muhammadu Sanusi II, ya shirya yin hawan salla a bana.
Sarkin ya jaddada cewa bikin hawan salla ba abu ne da ya zama wajibi ba idan zai iya haddasa rikici da asarar rayuka.
“Idan akwai fargabar cewa hawan salla zai haddasa tashin hankali da asarar rayuka ko dukiyoyi, to, yana da kyau a daina,” in ji shi.
A gefe guda, al’ummar Kano sun nuna damuwa kan yadda rikicin masarautar ke ci gaba da yin tasiri a rayuwarsu.
Ana sa ran wannan matakin zai rage fargabar da ake ciki, tare da tabbatar da zaman lafiya a Jihar Kano.