Shugaban kungiyar ‘al-Hikimah” na kasar Iraki Ammar Hakim ya gana da shugaban kasar Masar Abdulfattah al-sisi. A yayin ganawar  Ammar Hakim ya jaddada muhimmancin taimaka wa kokarin da Masar take yi na ganin an hana korar falasdinawa daga yankunansu zuwa wajen Falasdinu.

Ammar Hakim ya kuma ce, a yayin wannan ganawar na bayyana wa shugaban kasar jinjinawarmu akan yadda Masar ta kasance mai taimaka wa Falasdinawa.

Haka nan kuma mun nuna goyon bayanmu ga kokarin Masar al’umma da gwamnati na hana tilasatawa Falasdinawa yin hijira da kuma kare hakkokin Falasdinawa da riko da kasarsu.

Har ila yau Ammar Hakim ya ce ganawar tasu ta tabo batutuwa da su ka shafi halin da ake ciki a wannan yankin da kuma wajabcin aiki a tsagaita wutar yaki a yankin Gaza.

Sayyid Ammar Hakim ya kuma yi ishara da muhimmanci sake gina yankin na Gaza ba tare da an fitar da mazaunansa daga ciki ba. Bugu da kari bangarorin biyu sun jaddada muhimmanci kafawa Falasdinawa daularsu akan iyakokin 1967 da birnin Kudus zai zama babban birninta domin haka ne hanyar samar da zaman lafiya a cikin wannan yankin.

Akan halin da ake ciki a matakin wannan yankin kuwa, Sayyid Ammar Hakim ya ce; Kasar Iraki tana son ganin an sami zaman lafiya a cikin wannan yankin da kuma warware sabanin da ake ciki a wannan yankin da kusanto da fahimtar juna a tsanakin bangarori mabanbanta.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Ammar Hakim ya wannan yankin

এছাড়াও পড়ুন:

Iran, Lebanon, Iraki, Yemen sun fara atisayen hadin gwiwa na goyan bayan Gaza

Kasashen Iran, Lebanon, Iraki, da kuma Yemen sun kaddamar da wani atisayen hadin gwiwa na sojojin ruwa domin nuna goyan baya ga  Falasdinawa a zirin Gaza, wadanda ke ci gaba da fuskantar zalinci  na gwamnatin Isra’ila.

An fara faretin hadin gwiwa a tekun Fasha, da yankin gabar tekun Makran, da kuma tekun Caspian da ke arewaci da kuma kudancin yankin ruwan Iran yau Alhamis gabanin ranar Qudus ta duniya.

Kwamandan rundunar sojojin ruwa na IRGC Rear Admiral Alireza Tangsiri ya ce jiragen ruwa masu nauyi da marasa nauyi 3,000 ne ke halartar faretin.

Ya kara da cewa, faretin na da nufin nuna karfin ruwa na bangaren ‘yan gwagwarmaya da kuma isar da sako ga miyagu da azzalumar gwamnatin Isra’ila.

A yayin faretin, an nuna tutar Falasdinu, sannan aka kona tutar Isra’ila a mashigin tekun Farisa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wakilin Sin: Dole Ne A Mutunta Hakki Mai Tushe Na Palasdinawa
  • Iran, Lebanon, Iraki, Yemen sun fara atisayen hadin gwiwa na goyan bayan Gaza
  • Nijar : An nada Janar Tiani, a mukamin shugaban rikon kwarya
  • HKI Ta Kai Hare-hare A Falasdinu Da Kasar Lebanon
  • Duniyarmu A Yau: Ranar Qudus Ta Duniya Ta Shekara 1446
  • Sin Na Ci Gaba Da Kasancewa Cibiyar Rarraba Hajojin Da Masana’antu Ke Sarrafawa
  • Iran Ta Turkiyya Sun Bukaci kasashen Musulmi Su Magance matsalar Jinkai A Kasar Palasdinu Da Aka Mamaye
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Zargin Kasar Amurkan Dangane Da Kamfanonin Man Fetur Na Kasar Ba Gaskiya Bane
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI
  • SDP: Ba Mu Yi Wa Kowa Alƙawarin Takarar Shugaban Ƙasa Ba