Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana cewa; Babu yadda za a yi mu zauna kan teburin tattaunawa da mutumin da yake fitowa fili yana yi mana barazana, kuma ya sa hannunsa a wuyansa ya sheke mu.

Shugaban kasar ta Iran wanda ya gana da ‘yan majalisa masu wakiltar gundunar Hamadan a daren jiya Litinin ya ce;  Mu mutane ne da mu ka yarda da tattaunawa,kuma a halin yanzu abinda ministan harkokin wajen Iran Abbas Arakci yake yi kenan da kasashen makwabta.

Da ya tabo batun takunkuman da Amurka take kakaba wa Iran kuwa, shugaban kasar ta Iran  ya ce, babu yadda za a yi a kakaba takunkumin ya yi tasiri akan kasar da take da iyaka mai tsawo da kasashe masu yawa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Yi Barazana Ga Ukraine A Dai-dai Lokacinda Ta Fitar Da Shirin Zaman Lafiya Da Rasha Na Karshe

Gwamnatin kasar Amurka ta gargadi kasar Ukraine a dai dai lokacinda ta gabatar da shirin zaman lafiya da kasar Rasha na karshe.

Shirin da shugaban kasar Donal Trump ya bayyana shi ne karshe dai, ya bukaci gwamnatin shugaba Volodimir Zelesky ta amince da yankin Cremea da kuma sauran yankunan hudu wadanda Rasha ta mamaye da karfi shekaru uku da suka gabata su zama mallakin kasar Rasha har’ abada. Sannan ta amince a daukewa kasar Rasha takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata tun bayan fara yakin. Sannan daga karshe ta amince ba zata shiga kungiyar tsaro ta NATO ba.

Shawara bata yi maganar wani abu banada wadannan hudu ba, duk da cewa Ukraine tana da wasu bukatu a yarjeniyar tsagaita wuta da kuma samar da sulhu mai dorewa.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa Moscow ta bukaci a tsagaita wuta tsakanin bangarorin biyu don samun damar tattaunawa amma gwamnatin Kiev ta ki amincewa.

Masana suna ganin wadannan al-amura suna da nauyi ga kasar ta Ukraine, amma kuma bata da zabi tunda Amurka ce ta biya mafi yawan kudaden da Ukraine ta kashe a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Yi Barazana Ga Ukraine A Dai-dai Lokacinda Ta Fitar Da Shirin Zaman Lafiya Da Rasha Na Karshe
  • Faransa ta jaddada aniyarta na ci gaba da tattaunawar nukiliyar iran
  • Sin Ta Musanta Yin Shawarwari Ko Tattaunawa Da Amurka Kan Batun Harajin Kwastam
  • Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita
  • Iran ta jinjinawa Sin da Rasha a matsayin kawayenta na kut-da-kut
  • Gwamna Inuwa Ya Bayar Da Gudunmawar Naira Miliyan 10 Ga Iyalan Wadanda Hatsarin Ista Ya Rutsa Da Su A Gombe
  • Xi: Yake-yaken Haraji Da Kasuwanci Na Tauye Hakkoki Da Muradun Dukkan Kasashe
  • Arakci: Mun Yi Tattaunawa Mai Kyau Da Mahukuntan Kasar China
  • Iran ta jaddada cewa: Ba Zata Taba Amincewa Da Gudanar Da Tattaunawa Kan Tsaronta Ba
  • Amurka ta kakaba wa Iran sabbin takunkumai duk da tattaunawa