Waɗanda Suka Yi Nasara

1. Aliyu Usman Adam – Matsayi na Ɗaya

Aliyu Usman Adam, ɗan asalin Zariya, Jihar Kaduna, an haife shi a shekarar 1984. Ya kammala karatunsa na firamare da sakandare a Zariya, sannan ya samu digiri a harshen Hausa daga Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya, a 2008. Bayan hidimar ƙasa a Jihar Edo, ya yi aiki a kamfanin SAN Yoghurt da kuma Alhuda Center School daga 2011 zuwa 2014.

A 2014, Aliyu ya koma aikin jarida, inda ya yi aiki da jaridar RARIYA a Abuja har zuwa 2017. A halin yanzu, shi ne Manajan shirye-shirye (Content Manager) a Nishadi TV Abuja. Yana da mata da ‘ya’ya biyu.

2. Zainab Muhammad (Indian Girl) – Matsayi Na Biyu

Zainab Muhammad, wacce aka fi sani da “Indian Girl,” ‘yar asalin ƙaramar hukumar Dala ce a Kano. Ta kammala firamare da sakandare a Kano, tare da burin ci gaba da karatun jami’a a nan gaba.

Zainab tana da ƙwazo a ɓangaren ilimin addinin Musulunci, kuma tana amfani da kafafen sada zumunta wajen ilmantarwa da faɗakarwa. A halin yanzu tana da tarin masoya saboda rubuce-rubucenta masu ƙayatarwa da gina al’umma.

3. Mujaheed Nuhu Yusuf (Mujaheed Matashi) – Matsayi Na Uku

Mujaheed Nuhu Yusuf, wanda aka fi sani da Mujaheed Matashin marubuci ne a fagen wasan kwaikwayo kuma mawaki daga Kano. Ya wallafa littattafai biyu na waƙoƙi, ciki har da Philosophy Mysterious Pen, wanda ya wallafa tare da marubuci Haiman Ra’ees.

Mujaheed shi ne shugaban ƙungiyar marubuta Ruhin Adabi, kuma yana wallafa rubuce-rubucensa a shirin Bakandamiya Hikaya da kuma shafinsa na Facebook.

Wannan gasa ta ƙara tabbatar da aniyar LEADERSHIP HAUSA na bunƙasa haɗaka da ƙirƙirar rubutu a cikin al’ummar Hausawa.

Jaridar na shirin ci gaba da shirya irin waɗannan gasar domin ƙarfafa sha’awar adabi da kuma ƙarfafa dangantaka da masu karatu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gajerun Labari

এছাড়াও পড়ুন:

Hadimin Gwamnan Kano Tanka Galadanci ya rasu

Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Rediyo ga Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasu.

Ya rasu ne a ranar Laraba 26 ga watan Maris, 2025, bayan gajeriyar rashin lafiya a Asibitin Koyarwa na Malam Aminu Kano.

Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4 Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojoji

Kakakin Gwamnan Kano, Sunusi Bature Dawakin Tofa ne ya tabbatar da rasuwar cikin wata sanarwa da ya fitar.

Sanarwar ta bayyana marigayin a matsayin ƙwararren ɗan jarida da ya taka rawar gani wajen inganta harkokin sadarwa a jihar.

Za a yi jana’izarsa da misalin ƙarfe 5:30 na yammacin yau Laraba a Filin Masallacin Galadanchi da ke kusa da gidan Galadiman Kano.

Gwamna Abba Kabir Yusuf, ya nuna alhininsa kan rasuwar Galadanci, tare da bayyana irin rawar da ya taka a gwamnatinsa.

“Rasuwar Abdullahi Tanka Galadanci babban rashi ne ga gwamnatina da Jihar Kano baki ɗaya.

“Za a yi rashinsa saboda jajircewarsa da ƙwazon da ya nuna wajen inganta harkokin sadarwarmu,” in ji gwamnan.

Ya kuma miƙa ta’aziyyarsa ga iyalansa, ’yan uwa da abokan arziƙi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Sudan Suna Ci Gaba Da Samun Nasara A Akan Dakarun Kai Daukin Gaggawa
  • NAJERIYA A YAU: Halin Da Matasa Suka Tsinci Kansu A Najeriya
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [19]
  • Hadimin Gwamnan Kano Tanka Galadanci ya rasu
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun sallaGwamnati Ta Ayyana 31 Ga Maris Da 1 Ga Afrilu A Matsayin Ranakun Hutu Don Bukin Eid-el-Fitr Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hu
  • Gidauniyar Daily Trust da WRAPA sun ’yanta fursunoni 21 a Kaduna da Katsina
  • Rikicin Masarauta: Duk mai ja da hukuncin Allah ba zai yi nasara ba — Sanusi II
  • Jarumin Kannywood Baba Ƙarƙuzu ya rasu
  • Super Eagles ta gamu da cikas a ƙoƙarin neman tikitin Gasar Kofin Duniya
  • Fursunoni 12 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Jihar Kogi