Aminiya:
2025-03-27@22:53:52 GMT

Manoman tumatir na tafka asara saboda faɗuwar farashi

Published: 25th, February 2025 GMT

Yayin da aka fara tsinkar tumatari dan rani a Kano da sauran jihohin da ke samar da tumatar a fadin Nijeriya, rahotanni sun bayyana cewa, farashinsa ya fadi sosai fiye da yadda aka yi zato, lamarin da ya jefa manoman cikin damuwa.

Binciken da Jaridar Aminiya ta gudanar ya nuna cewa, a halin yanzu, ana sayar da kwando daya na tumatir a kan Naira 3,500, yayin da ake sayar da babban kwando a kan Naira 10,000.

40% na matan Kano sun fuskaci cin zarafi a gida —Shugaban Majalisa Dan kwallon Najeriya ya mutu bayan fadowa daga bene a Uganda

Wani manomin tumatir, Isah Bello Abba ya bayyana cewa, wannan yanayi ya sa manoma cikin fargaba saboda sun kashe kudade masu yawa wajen noman tumatir na rani, amma yanzu suna fuskantar yiwuwar yin babbar asara.

“Mun zuba jari mai yawa a bana, amma daga dukkan alamu, ba za mu samu riba mai yawa ba. Wannan yanayi yana tsoratarwa, kuma muna fatan abubuwa za sudaidaita nan gaba,” in ji shi.

Shugaban Kungiyar Tomato Out Growers Association of Nigeria (TOGAN) reshen Jihar Kano, Alhaji Sani Danladi Yadakwari, ya bayyana cewa, tabbas wannan yanayi abin damuwa ne, musamman ma tunda yanzu ne farkon kakar, ba lokacin kololuwa ba.

Ya ce, kungiyar ta fahimci matsalar kuma tana aiki tare da Gwamnatin Tarayya don ganin an dauki matakan da za su tallafa wa manoman, inda ya tabbatar cewa, nan ba da dadewa ba za a fito da tsarin magance matsalar.

A cewarsa, ɗaya daga cikin hanyoyin magance matsalar ita ce kafa kananan masana’antu na sarrafa tumatir a fadin kasa, wanda zai rage yawan asarar da ake samu yayin girbi da kuma karancin farashi a kasuwa.

Ya yi kira ga masu ruwa da tsaki a bangaren kasuwanci da su fara kafa irin wadannan masana’antu domin bunkasa tattalin arziki da rage radadin da manoma ke fuskanta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: farashi

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun sallaGwamnati Ta Ayyana 31 Ga Maris Da 1 Ga Afrilu A Matsayin Ranakun Hutu Don Bukin Eid-el-Fitr Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hu

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Litinin, 31 ga watan Maris, da Talata, 1 ga watan Afrilu, a matsayin ranakun hutun ƙaramar salla.

Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da sakataren ma’aikatar, Magdalene Ajani, ya fitar a ranar Laraba.

Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe Tsohon hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasu

Ya taya al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan cikin nasara, tare da yin kira a gare su da su ci gaba da halaye nagari da suka koya a watan.

Haka kuma ya jaddada muhimmancin soyayya, yafiya, da haɗin kai wajen gina al’umma.

Tunji-Ojo, ya buƙaci ’yan Najeriya da su yi amfani da wannan lokaci wajen yin addu’a domin samun zaman lafiya, kwanciyar hankali, da ci gaban ƙasa.

Ya yi fatan cewa bukukuwan salla za su ƙara haɗin kai tsakanin mutane duk da bambancin addini da ƙabilanci da ake da su.

Haka kuma, ya yi kira ga jama’a da su yi bukukuwan ta hanyar tunawa da mabuƙata, ta yadda za a taimake su.

A madadin Gwamnatin Tarayya, ministan ya aike da saƙon fatan alheri ga dukkanin Musulmi tare da addu’ar Allah Ya sanya farin ciki a zukatan kowa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Miliyoyin  ‘Yahudawa Sun Gudu Neman Mafaka Saboda Makamin Mai Linzami Daga Yemen
  • Sarkin Kano Na 15 Ya Soke Hawan Daba Saboda Matsalar Tsaro
  • Hadimin Gwamnan Kano Tanka Galadanci ya rasu
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun sallaGwamnati Ta Ayyana 31 Ga Maris Da 1 Ga Afrilu A Matsayin Ranakun Hutu Don Bukin Eid-el-Fitr Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hu
  • Jagoran Juyin Musulunci Ya Amince Da Yin Afuwa Ga Wasu Fursunoni Masu Yawa
  • Tsohon hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasu
  • Ban taɓa fuskantar tsangwama a Kannywood ba — Prince Aboki
  • Araqchi: Har yanzu Iran ba ta mayar da amsa ga wasikar Trump kan tattaunawar nukiliya ba
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [17]