Aminiya:
2025-04-25@17:53:58 GMT

Manoman tumatir na tafka asara saboda faɗuwar farashi

Published: 25th, February 2025 GMT

Yayin da aka fara tsinkar tumatari dan rani a Kano da sauran jihohin da ke samar da tumatar a fadin Nijeriya, rahotanni sun bayyana cewa, farashinsa ya fadi sosai fiye da yadda aka yi zato, lamarin da ya jefa manoman cikin damuwa.

Binciken da Jaridar Aminiya ta gudanar ya nuna cewa, a halin yanzu, ana sayar da kwando daya na tumatir a kan Naira 3,500, yayin da ake sayar da babban kwando a kan Naira 10,000.

40% na matan Kano sun fuskaci cin zarafi a gida —Shugaban Majalisa Dan kwallon Najeriya ya mutu bayan fadowa daga bene a Uganda

Wani manomin tumatir, Isah Bello Abba ya bayyana cewa, wannan yanayi ya sa manoma cikin fargaba saboda sun kashe kudade masu yawa wajen noman tumatir na rani, amma yanzu suna fuskantar yiwuwar yin babbar asara.

“Mun zuba jari mai yawa a bana, amma daga dukkan alamu, ba za mu samu riba mai yawa ba. Wannan yanayi yana tsoratarwa, kuma muna fatan abubuwa za sudaidaita nan gaba,” in ji shi.

Shugaban Kungiyar Tomato Out Growers Association of Nigeria (TOGAN) reshen Jihar Kano, Alhaji Sani Danladi Yadakwari, ya bayyana cewa, tabbas wannan yanayi abin damuwa ne, musamman ma tunda yanzu ne farkon kakar, ba lokacin kololuwa ba.

Ya ce, kungiyar ta fahimci matsalar kuma tana aiki tare da Gwamnatin Tarayya don ganin an dauki matakan da za su tallafa wa manoman, inda ya tabbatar cewa, nan ba da dadewa ba za a fito da tsarin magance matsalar.

A cewarsa, ɗaya daga cikin hanyoyin magance matsalar ita ce kafa kananan masana’antu na sarrafa tumatir a fadin kasa, wanda zai rage yawan asarar da ake samu yayin girbi da kuma karancin farashi a kasuwa.

Ya yi kira ga masu ruwa da tsaki a bangaren kasuwanci da su fara kafa irin wadannan masana’antu domin bunkasa tattalin arziki da rage radadin da manoma ke fuskanta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: farashi

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita

Jamhuriyar Musulunci ta Iran Ta bayyana cewa; Kakaba takunkumi kan kasarta ya sabawa ikirarin Amurka na yin shawarwari da ita

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baqa’i ya yi kakkausar suka kan matakin da Amurka ta dauka na kakabawa wasu gungun mutane masu alaka da bangaren makamashi, man fetur da iskar gas da kuma wasu mutane da dama masu fafutuka a shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran na lumana takunkumi.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Baqa’i ya bayyana manufar takunkuman da Amurka ta kakabawa al’ummar Iran da cewa; A fili take nuna kyama ga masu yanke shawaran Amurka kan al’ummar Iran da kuma nuna rashin mutunta doka da hakkin dan Adam ne.

Ya kara da cewa: Dogaro da tsarin gwamnatocin Amurka da suka shude kan takunkumin tattalin arziki a kan kasashe masu tasowa, a matsayin makamin tsoratarwa da matsin lamba na siyasa, wani lamari ne da ya saba wa muhimman ka’idojin Yarjejeniya ta Majalisar Dinkin Duniya da kuma dokokin kasa da kasa, kuma yana yin zagon kasa ga ginshikin doka da ka’idojin ciniki cikin ‘yanci, kuma yana haifar da keta hakkin bil’adama na asali na al’ummomin da takunkumin ya shafa, musamman ‘yancin ci gaba. Wannan hali sau da yawa yana zama laifi ga ɗan adam.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Shirin Tsaftar Muhalli Na Wata Wata Saboda Jarrabawar JAMB
  • Idan Kana Son Barin PDP, Yanzu Ne Lokacin – Bukola Saraki
  • Ficewar Kawu a jam’iyyarmu zai kawo zaman lafiya – Shugaban NNPP na Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Soke Tsaftar Muhalli A Watan Afrilu Saboda Jarabawar JAMB
  • Kasar Iran Ta Bayyana Cewa Kakaba Takunkumi Kan Kasarta Ya Sabawa Hikimar Gudanar Da Zaman Tattaunawa Da Ita
  •  WHO: Masu Ciwon Koda 400 A Gaza Sun Mutu Saboda Rashin Magani
  • Yanzu-yanzu: Gwamnan Delta Oborevwori Ya Fice Daga PDP Zuwa APC
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana China Da Rasha A Matsayin Abokai Na Tushe Ga Iran
  • Dakarun IRGC Suna Cikin Shirin Ko Ta Kwana Don Kare JMI Daga Makiyanta
  • ECOWAS Zata YI Taro A Ghana Don Tattauna Batun Niger, Mali Da Burkina Faso