Aminiya:
2025-02-25@22:17:56 GMT

An naɗa Obasanjo mai shiga tsakani a rikicin Kongo

Published: 25th, February 2025 GMT

An naɗa wasu dattawan Afirka da suka yi mulki a ƙasashen yankin a matsayin masu shiga tsakani domin warware takaddamar da ta ɓarke a tsakanin ’yan tawayen M23 da gwamnatin Dimokuraɗiyyar Kongo.

Ƙungiyoyin raya ƙasashen gabashi (EAC) da kudancin nahiyar Afirka (SADC) ne suka naɗa tsoffin shugabannin Habasha da Kenya da Nijeriya domin sanya idanu a kan batun sulhu a Jamhuriyyar Dimokuraɗiyyar Kongo inda yaƙi ya ƙazanta a gabashin ƙasar.

Manoman tumatir na tafka asara saboda faɗuwar farashi 40% na matan Kano sun fuskaci cin zarafi a gida —Shugaban Majalisa

Shugabanin ƙasashen gabashi da kudanci da ma yammacin Afirka ne suka yi naɗin a wani yunƙuri na kawo ƙarshen yaƙin basasa a gabashin Kongo, tare da cimma matsaya kan batun yarjejeniyar samar da zaman lafiya a tsakanin ’yan tawaye da gwamnatin Kinshasa ke zargi na samun goyon bayan Rwanda da hukumomi na gwamnatin tsakiya.

Da yammacin jiya Litinin, suka fitar da sanarwar cewa sun naɗa tsohon shugaban Kenya, Uhuru Kenyatta da tsohon Firai Ministan Habasha, Hailemariam Desalegn da kuma tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo a matsayin waɗanda za su taimaka wajen aiwatar da sabuwar yarjejeniyar sulhu.

“An buƙaci dukkan ɓangarorin su mutunta tsagaita wutar da aka ayyana a taron EAC da SADC, kuma an yi kira ga M23 da kuma sauran ɓangarorin su dakatar da kutsawa cikin gabashin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo tare da mutunta tsagaita wuta,” in ji ƙungiyoyin a wata sanarwar da suka fitar.

Har yanzu ƙungiyoyin kasa da kasa da suka haɗa da Majalisar Dinkin Duniya da Ƙungiyar Tarayyar Afirka ta AU sun gaza shawo kan rikicin na Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kongon wanda ya laƙume rayukan fararen hula da dama.

Yaƙi a gabashin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo ya yi sanadiyyar mutuwar mutum fiye da 7,000 a wannan shekarar, kamar yadda Firaiministar ƙasar Judith Suminwa Tuluka ta shaida wa kwamitin kare haƙƙin ɗan’adam na Majalisar Ɗinkin Duniya ranar Litinin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Uhuru Kenyatta

এছাড়াও পড়ুন:

Arewa na buƙatar haɗa kai da Kudu Maso Kudu don ceto Najeriya — El-Rufai

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya buƙaci manyan ‘yan siyasa daga yankin Arewa da Kudu Maso Kudu su haɗa kai gabanin zaɓen 2027.

El-Rufai, ya yi wannan kira ne yayin da ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan marigayi dattijo kuma jagoran yankin Neja Delta, Edwin Clark.

Babu ɗan Arewa mai hankali da zai yi tallan APC a 2027 – Jigo a PDP Fasinjoji 4 sun rasu yayin da bas ta kama da wuta a Jigawa

A cewarsa, Najeriya tana cikin matsala mai tsanani kuma tana buƙatar ɗauki cikin gaggawa.

“A shekarun baya, Arewa da Kudu Maso Kudu sun kasance abokan siyasa,” in ji El-Rufai.

“Kada mu manta da hakan. Mu koma kam wannan haɗin kai. Mu ceci wannan ƙasa domin tana buƙatar ceton gaggawa. Dole ne mu ɗauki matakin ceton ƙasar nan.”

Maganganunsa sun zo ne yayin da ake raɗe-raɗin cewa yana shirin sauya sheƙa daga jam’iyyar APC.

A makonnin da suka gabata, ya gana da ’yan siyasa daga jam’iyyun adawa bayan wani saɓani tsakaninsa da jam’iyyar APC mai mulki da kuma gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

El-Rufai, wanda ya je ziyarar ta’aziyyar tare da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya yaba da rawar da Atiku ya taka wajen kawo sauye-sauyen tattalin arziƙi a lokacin mulkin Shugaba Olusegun Obasanjo.

Segun Showunmi, tsohon mai magana da yawun yaƙin neman zaɓen Atiku, ya tabbatar da cewa wannan ganawar tana cikin shirye-shiryen siyasa gabanin zaɓen 2027.

A watan Janairu, El-Rufai ya gana da Hamza Al-Mustapha, tsohon hadimin marigayi Janar Sani Abacha, da Shehu Gabam, shugaban jam’iyyar SDP, da wasu ’yan siyasa a Abuja.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministar Wajen Madagascar: Muna Godiya Ga Tawagogin Likitanci Na Sin
  • Mutum 7,000 Suka Mutu A Rikicin Gabashin Kwango Tun Daga Watan Janairu
  • MDD : Kwamitin Sulhu ya amince da kudurin Amurka kan rikicin Rasha da Ukrain
  • Ba ni lokacin cacar baka da El-Rufai —Nuhu Ribadu
  • Rasha : Putin Ya Ce Turawa ‘Na Iya Shiga’ A Sasanta Rikicin Ukraine
  • Xi Ya Tattauna Da Putin Ta Wayar Tarho 
  • Arewa na buƙatar haɗa kai da Kudu don ceto Najeriya — El-Rufai
  • Arewa na buƙatar haɗa kai da Kudu Maso Kudu don ceto Najeriya — El-Rufai
  • Wang Yi Ya Yi Bayani Kan Ziyararsa A Birtaniya Da Ireland Da Halartar Taron Kolin Kwamitin Sulhu Da Na Tsaro A Munich Da Na G20