An gurfanar da wadanda ake zargin ne bisa laifuka daban-daban, da ke da alaka da laifukan zamba ta yanar gizo, mallakar wasu takardu da ke dauke da shaidar karya, da kuma satar bayanan sirri.

 

Dukkansu sun ki amsa laifin da ake tuhumar su da su a lokacin da aka karanta musu tuhumar, sai dai lauyan masu shigar da kara, Nnaemeka Omewa, ya bukaci kotun da ta dage zaman shari’ar tare da tsare wadanda ake kara a gidan gyaran hali.

 

Mai shari’a Osiagor ya dage sauraron karar zuwa ranar 23 ga watan Yunin 2025 domin ci gaba da shari’a, sannan ya bayar da umarnin a tsare su a gidan gyaran hali.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin

Majiyar asibiti a yankin Gaza, ta ambaci cewa an sami karuwar shahidai a cikin sassa mabanbanta na zirin Gaza zuwa 38, 3 daga cikinsu a yankin Deir-Balah.

Jiragen yakin HKI sun kai wasu hare-hare akan wata mota da take dauke da wasu ‘yan’uwa shakikai su 6, da hakan ya yi sanadiyyar shahadarsu baki daya.

‘Yan’uwan 6 da su ka yi shahadai, suna aiki ne da wata kungiyar agaji da take rabawa ‘yan hijira kayan abinci da sauran na bukatunsu na yau da kullum.

Sojojin HKI sun fitar da wata sanarwa da a ciki su ka riya cewa, wadanda su ka kai wa harin suna Shirin kai musu hari ne.

A jiya Litinin da marece sojojin HKI sun rushe wasu gidaje a yammacin garin Rafah a kudancin zirin Gaza.

A yammacin sansanin ‘yan hijira dake yammacin Khan-Yunus, jirgin sama maras matuki na HKI ya kai hari da hakan ya yi sanadin shahadar mutane biyu,kmar yadda su ka kashe shugaban ‘yan sandan yankin yammacin Khan-Yunus.

Wata sanarwa ta rundunar sojan HKI ta ce, a cikin kwanaki biyu da su ka gabata sun kai hare-hare ta sama har sau 90 a fadin yankin Gaza.

A wani labarin na daban, sojojin HKI sun gargadi mazauna unguwanni daban-daban a kudancin Khan-Yunus da su fice daga cikinsu, saboda za su rusa su. Unguwannin da gargadin ya shafa sun hada Qizan-al-Najjar, Abu Rashwan, Assalam da Manarah. Sai kuma unguwannin Qarin, Ma’an, Batan-al-Yasmin da Fakhari. Haka nan kuma Bani Suhailah ta kudu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar EFCC Ta Kama Mutane 40 da Ake Zargi da Damfarar Intanet
  • Zargin Ganduje: Za mu sanar da lokacin yanke hukunci —Kotu
  • EFCC Ta Kama Wasu Mutane 40 Da Ake Zargi Da Yin Damfara Ta Intanet A Neja
  • Shugaba Xi Ya Yi Kira Ga Sin Da Vietnam Da Su Wanzar Da Daidaito A Tsarin Rarraba Hajoji
  • EFCC ta gaza tabbatar da tuhumar Murja kan zargin wulaƙanta takardar Naira
  • EFCC Ta Gurfanar Da Ɗan China A Kotu Kan Bayar Da Bayanan Ƙarya
  • An Kashe Sojojin Yahudawa A Gaza A Yayinda Wasu Da Dam Suka Ji Rauni
  • Kotu ta tsare ’yan TikTok 2 a Kano
  • Gaza: Mutane 38 Sun Yi Shahada A Yau Litinin
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe