Shugaban Zimbabwe Ya Kaddamar Da Yankin Masana’antu Da Sin Ta Zuba Jari
Published: 25th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa a ranar Litinin ya halarci bikin kaddamar da gina yankin masana’antu da kasar Sin ta zuba jari, inda ya bayyana shi a matsayin wani ci gaba na bunkasa masana’antu a kudancin Afirka.
Kamfanin Xintai Resources na kasar Sin ne ya zuba jarin dala biliyan 3.6 a yankin masana’antu musamman na makamashi da karafa na kogin Palm da ke Beitbridge na lardin Matabeleland ta kudu, kuma za a aiwatar aikin a matakai biyar cikin shekaru 12, da nufin samar da kayayyakin da ake amfani da su na chromium da coke.
Mnangagwa ya ce, “Ina fatan aikin wannan yankin masana’antu na musamman, zai taka rawa a matsayin wani muhimmin tubali ga ci gaban masana’antu da zamanantar da al’ummarmu. Muna sa ran wannan aikin zai taimaka wajen ciyar da tattalin arzikin kasarmu gaba da kuma bude hanyoyin da ba a taba ganin irinsu ba wajen samar da ayyukan yi, da ci gaban fasaha, da ci gaban zamantakewa,”
Ya ce, aikin wani babban ci gaba ne ga hanyar da Zimbabwe ke bi wajen bunkasa masana’antu saboda ya hada aikin samar da makamashi da karafa, bangarori biyu masu muhimmanci da ke da damar sake fayyace yanayin masana’antu na kasar. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ba a taɓa Dimokraɗiyya mai tsafta a Najeriya kamar mulkin Tinubu ba – Matawalle
Karamin Ministan Tsaro a Najeriya Bello Matawalle, ya caccaki masu sukar lamirin Shugaban Kasa Bola Tinubu game da nuna wariya ga yankin Arewacin Najeriya.
Matawalle ya ce Tinubu kadara ne ga Arewa kuma ba shi da fatan da ya wuce ganin ya magance matsalolin da suka addabi yankin kafin 2027.
Cikin wani jawabi da mai taimaka masa kan sha’anin siyasa Ibrahim Danmaliki Gidan Goga ya fita, Matawalle ya ce ba a taba samun lokacin da ake yin dimokradiyya mai tsafta kamar a zamanin Bola Tinubu ba.
’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista
Ya ce duk masu kushe salon mulkinsa kawai suna huce haushin rashi ne da yada farfaganda da karairayi.
“Mutanen Arewa suna da wayewar da sun fi karfin a yaudare su domin cimma wata manufar siyasa. Akwai bukatar mu hada kai waje daya kada mu yarda a yaudare mu.” Inji Matawalle.
Ministan ya ce kamata ya yi a gode ma Tinubu saboda yadda yake inganta yankin Arewa da tsaro kuma ana ganin ci gaba musamman yankin da ya fito na Sokoto-Kebbi-Zamfara.
Bugu da kari ya yaba ma ayyukan ci gaban da yake kawo wa yankin musamman yadda ake shimfida tituna da kokarin kawo ci gaba ga yankin.