Babu hannun Naira Marley a mutuwar Mohbad — Kotu
Published: 25th, February 2025 GMT
Kotun Majistire da ke zama a Sabo a unguwar Yaba ta Jihar Legas ta wanke mawaƙi Abdulazeez Fashola, wanda aka fi sani da Naira Marley da abokin aikinsa Samson Balogun Eletu, wato Sam Larry daga zargin hannu a mutuwar mawaƙi Aloba Oladimeji IleriOluwa, wanda aka fi sani da Mohbad.
Mai Shari’a Ejiro Kubenje, wanda ya karanta hukuncin ya ce babu wata ayar tambaya kan mutanen biyu game da rasuwar Mohbad.
Haka nan ma kotun ta sallami Oodunni Ibrahim, wanda ake kira Primeboy da tsohon manajan Mohbad, Opere Babatunde.
Sai dai hukuncin ya ce za a gurfanar da ma’aikaciyar jinyar da ta kula da Mohbad gabanin mutuwarsa, wato Feyisayo Ogedengbe, da ɗaya daga cikin abokan marigayin, Ayobami Sadiq bisa tuhumar su da sakaci, wanda ya kai ga mutuwar matashin mawaƙin.
Ana iya tuna cewa, mutuwar Mohbad a shekarar 2023 dai ta janyo ce-ce-ku-ce matuƙa musamman a kafafen sada zumunta na zamani a ciki da wajen Nijeriya.
Kazalika, a wancan lokacin an gudanar da zanga-zanga a jihohin Legas da Oyo da Delta, don neman a binciki musabbabin mutuwar ta shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Naira Marley
এছাড়াও পড়ুন:
Babu ɗan Arewa mai hankali da zai yi tallan APC a 2027 – Jigo a PDP
Jam’iyyar adawa ta PDP ta bayyana cewa babu wani ɗan Arewa mai mai hankali da zai goyi bayan APC a zaɓen 2027.
PDP ta bayyana hakan ne a matsayin martani kan zargin cewa Sanata Lawal Adamu, Sanata mai wakiltar Kaduna ta Tsakiya, baya aikin komai sai ɗumama kujera.
Fasinjoji 4 sun rasu yayin da bas ta kama da wuta a Jigawa Gawuna ne ya lashe zaɓen Gwamnan Kano a 2023 — AtaHaka kuma, ana zargin gwamnatin Jihar Kaduna da dakatar da rarraba kayayyakin koyarwa da Sanata Lawal Adamu ya saya domin amfanin makarantun jihar.
Yusuf Dingyadi, Mataimaki na Musamman na Shugaban PDP kan Yaɗa Labarai, ya ce ya kamata gwamnatin jihar ta haɗa kai da wakilan jama’a don ci gaban al’umma.
“Abin da ake buƙata shi ne gwamnatin jihar, ba tare da la’akari da bambancin siyasa ba, ta haɗa kai da sauran wakilan jama’a don inganta rayuwar al’ummar Kaduna.
“PDP jam’iyya ce mai aƙida, kuma idan har kuna ci gaba da kai mata hari, ba za ku taɓa samun ci gaba ba.
“Ba za ku iya ɗaukar ’yan daba da masu yaɗa farfaganda don ɓata mana suna ba, kawai don ku burge Shugaba Bola Tinubu saboda burinku na 2027.
“Babu wani ɗan Arewa mai hankali da zai yi wa APC kamfe a Arewa.
“Gaskiyar ita ce, wasu ’yan siyasa suna yi masa biyayya ne ba don suna goyon bayansa da gaske ba, sai dai kawai don su samu abinci,” in ji shi.
Dingyadi ya shawarci Gwamna Uba Sani da kada ya bari wasu ’yan siyasa su ruɗe shi.
Ya ƙara da cewa, “’Yan majalisar da PDP ta zaɓa suna aiki tuƙuru. Suna yin ƙoƙari a yankunansu sama da na APC.
“Ba za ku iya daƙile nasarar siyasarmu ta hanyar ɗaukar ’yan farfaganda don su kai wa wakilanmu masu aiki hari ba, ko kuma ta hanyar shirya ficewar ’yan siyasa daga PDP a wuraren da aka shirya da gangan.”