Daliban mu Na Daf da Fara Kera Motoci – Farfesa Katsayal
Published: 25th, February 2025 GMT
Dalibban Jami’ar Sufuri ta Gwamnatin Tarayya dake Daura na daf da fara Jirage da Motoci
Shugaban Jami’ar Farfesa Umar Adam Katsayal ne ya bayyana haka lokacin da yake magana da Radio Nijeriya Kaduna a ofishinsa na Daura.
Ya kara da cewa Jami’ar Sufurin da Gwamnatin Tarayya ta Samar na da manufar Samar da dalibbai masu hazaka da zasu kasance masu kirkire kirkire da manufar ganin ana yaye dalibbai da zasu dogaro da kansu dama taimakawa wajen habakar tattalin arzkin kasa.
Shugaban Jami’ar Farfesa Umar Adam Katsayal ya Kara da cewa baya ga ilmantar da dalibbai Jami’ar tsaye take wajen ganin sun Samar da dalibbai masu tarbiyya da zasu kasance abin alfahari cikin al’umma.
Hakama Shugaban Jami’ar ya bayyana cewa yanzu haka dalibbai da suka fara karatu a Jami’ar na samun ingantaccen Ilmin Kimiyya da Fasaha da zasu kasance masu kirkire kirkire da nan gaba zasu kasance masu kawowa wannan kasa habakar tattalin arzkin baya ga dogaro da kansu da samarwa dinbin al’umma ayukkan yi.
Idris Kaurar Namoda
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Tawagar Iran a Beirut ta gana da shugabannin Lebanon
Tawagar gwamnatin Iran da ke ziyara a birnin Beirut domin halartar jana’izar shugabannin gwagwarmaya Sayyed Hassan Nasrallah da Sayyed Hashem Safieddine karkashin jagorancin shugaban majalisar dokokin kasar Mohammad Bagher Ghalibaf da ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi sun gana da shugaban kasar Labanon Joseph Aoun.
Bayan nan kuma tawagar ta gana da shugaban majalisar dokokin kasar Nabih Berri, sannan ta ci gaba da tattaunawa da sauran jami’ai da suka hada da firaministan kasar Labanon Nawaf Salam.
Ghalibaf da sauran jami’ai sun tafi kasar Lebanon a safiyar Lahadi don halartar jana’izar Sayyid Hassan Nasrallah, tsohon babban sakataren kungiyar Hizbullah, da kuma magajinsa Sayyed Hashem Safieddine, wadanda gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kashe su a karshen shekarar da ta gabata.
Da yake zantawa da manema labarai gabanin tafiyar tasa, Ghalibaf ya bayyana jana’izar a matsayin wani lokaci mai ma’ana ga kungiyar gwagwarmaya, duniyar musulmi, da kuma al’ummar Lebanon.
A lokacin da ya isa birnin Beirut babban jami’in na Iran ya bayyana Nasrallah a matsayin wani mutum mai babban matsayi kuma abin alfahari ga duniyar musulmi, yana mai jaddada abin da ya bari a matsayin wata alama ta tsayin daka a kan yakin kisan kare dangi na “Isra’ila” a Gaza.
Ghalibaf ya kara da cewa, duk da shahadarsu, amma Hizbullah da al’ummar Lebanon na alfahari da wadannan gwaraza.