Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da kudirin kasafin kudi na shekarar dubu biyu da ashirin da biyar na kananan hukumomi ashirin da uku a matsayin doka.

 

Shugaban Majalisar, Alhaji Yusuf Dahiru Liman, wanda ya jagoranci zaman, ya bayyana cewa an kara kasafin kudin zuwa sama da naira biliyan dari da ashirin da uku.

 

Yayin gabatar da kudirin a zauren majalisa don amincewa, Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi da Aiwatarwa, Yunusa Shehu Pambegua, ya bayyana cewa a baya bangaren zartaswa ya mika kasafin kudi na sama da naira biliyan dari da goma sha biyar na kananan hukumomi ashirin da uku na jihar.

 

 

Yunusa Shehu Pambegua ya bayyana cewa yayin kare kasafin kudinsu, shugabannin wasu kananan hukumomi sun nemi karin kudi don biyan bukatun ma’aikata da sauran kudaden gudanarwa.

 

Shugaban kwamitin ya ce bayan da shugabannin kananan hukumomi suka gabatar da yadda suka kashe kasafinsu kuma suka kare sabon kasafin, kwamitin ya gano cewa wasu kananan hukumomi suna bukatar gyara kasafinsu, kuma aka bukaci su rubuta hakan.

 

Ya ce an sake daidaita kasafin kudin tare da hadin gwiwar hukumomin da abin ya shafa, inda sabon jimillar kasafin kudin ya karu zuwa sama da naira biliyan dari da ashirin da uku, ciki wanda kashe kudin yau da kullum ya kai kashi sittin cikin dari, yayin da na ayyukan ci gaba ya tsaya a kashi arba’in cikin dari.

 

Yunusa Shehu Pambegua ya shawarci shugabannin kananan hukumomi da su yi amfani da kasafin kudin yadda ya kamata ta hanyar gudanar da mulki na kowa da kowa don amfanin daukacin al’ummar Jihar Kaduna.

 

‘Yan majalisar sun amince da kudirin ba tare da sabani ba bayan ya tsallake karatu na uku, kuma yanzu ana jiran amincewar gwamna domin ya zama doka.

 

Cov/Shamsudeen Manir Atiku

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki Ta Amince Da Kasafin Kudin

এছাড়াও পড়ুন:

KADGIS Ta Samar Da Sabuwar Manhajar Biyan Diyyar Filaye A Kaduna

Gwamna Uba Sani ya amince da sabon tsarin biyan  diyya ta hanyar amfani da fasahar zamani  ga Hukumar Kula da Bayanan Filaye ta Kaduna (KADGIS), da nufin dakile almundahana a harkokin biyan diyya na filaye a fadin jihar.

Daraktan Hukumar KADGIS Dr. Bashir Garba Ibrahim, ne ya bayyana hakan yayin da ya karbi bakuncin mambobin Kungiyar ‘Yan Jarida ta kasa (NUJ), rashen Rediyon Najeriya Kaduna, a ofishinsa da ke Kaduna.

Dr. Bashir Garba Ibrahim ya bayyana cewa wannan sabuwar manhaja za ta rika adana bayanan masu asalin filayen da za a biya diyya, da suka hada da daukar hoton ‘yan yatsun da lambar katinsu na dan kasa NIN, domin hana masu zamba karbar diyya akan filayen da ba nasu ba ne.

Haka zalika, Daraktan ya yi bayanin sauye-sauye da aka aiwatar a karkashin jagorancinsa tun bayan hawansa kan mukami.

Ya ce cikin shekaru biyu da suka gabata, KADGIS ta warware sama da kararrakin rikicin fili 700, tare da kaddamar da tsarin rangwamen kashi 20 bisa 100 ga wadanda suka biya dukkan bashin da ke kansu gaba daya, wanda hakan ya inganta samun kudaden shiga da inganta ayyuka matuka.

Dr. Bashir Garba ya tabbatar da cewa yanzu takardar mallakar fili (Certificate of Occupancy – C of O) tana cikin tsarin gaggawa, inda ake iya fitar da ita cikin sa’o’i 24 muddin dukkan sharudda sun cika, inda ake iya bayar da takardun shaidar mallakar sama da 200 a kowane mako.

A nasa jawabin, Shugaban NUJ reshen Rediyon Najeriya Kaduna, Umar Adamu S. Fada, ya yaba wa Daraktan da dukkan ma’aikatan hukumar bisa wadannan sauye-sauye, musamman na sabuwar manhajar  biyan diyya, da kuma hanzarta fitar da takardun shaidar mallaka.

Ya nuna farin ciki da damar hadin gwiwa a tsakanin bangarorin biyu, tare da bayyana shirin kungiyar na yin aiki tare da sashen hulda da jama’a na hukumar domin inganta samar da bayanai.

Kungiyar ta kuma yi tayin tallafawa hukumar, ta hanyar amfani da shirye-shiryen tasharsu don kara kusantar da jama’a ga ayyukan hukumar, da kara fadakar da su kan harkokin filaye a fadin jihar.

 

Umar S. Fada 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ya Yi Bikin Easter Tare da Al’ummomin Kiristoci
  • 2027: Dalilan Da Suka Sa ‘Yan Siyasa Ke Tururuwar Zuwa Gidan Buhari A Kaduna
  • Dokar-ta-baci: Shugaban Majalisar Wakilai Ya Gargadi Kantoman Ribas
  • ’Yan bindiga sun sace makiyaya 5, da shanu 1,200 a Kaduna
  • Hukumar Alhazai ta Jigawa Ta Shirya Bitar Ga Malaman Bita na Kananan Hukumomi 27
  • Majalisar Kasa Ta Rasha Ta Amince Da Yarjeniyar Dangantaka Ta Musamman Tsakanin Iran Da Kasar
  • Majalisar Dokokin Zamfara Ta Dawo da Dan Majalisa Basko da Aka Dakatar
  • WTO Ta Yi Gargadi Akan Karin Kudin Fito Na Amurka
  • KADGIS Za Ta Yi Amfani Da Sabuwar Manhajar Biyan Diyyar Filaye A Kaduna
  • KADGIS Ta Samar Da Sabuwar Manhajar Biyan Diyyar Filaye A Kaduna