Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta amince da kudirin kasafin kudi na shekarar dubu biyu da ashirin da biyar na kananan hukumomi ashirin da uku a matsayin doka.

 

Shugaban Majalisar, Alhaji Yusuf Dahiru Liman, wanda ya jagoranci zaman, ya bayyana cewa an kara kasafin kudin zuwa sama da naira biliyan dari da ashirin da uku.

 

Yayin gabatar da kudirin a zauren majalisa don amincewa, Shugaban Kwamitin Kasafin Kudi da Aiwatarwa, Yunusa Shehu Pambegua, ya bayyana cewa a baya bangaren zartaswa ya mika kasafin kudi na sama da naira biliyan dari da goma sha biyar na kananan hukumomi ashirin da uku na jihar.

 

 

Yunusa Shehu Pambegua ya bayyana cewa yayin kare kasafin kudinsu, shugabannin wasu kananan hukumomi sun nemi karin kudi don biyan bukatun ma’aikata da sauran kudaden gudanarwa.

 

Shugaban kwamitin ya ce bayan da shugabannin kananan hukumomi suka gabatar da yadda suka kashe kasafinsu kuma suka kare sabon kasafin, kwamitin ya gano cewa wasu kananan hukumomi suna bukatar gyara kasafinsu, kuma aka bukaci su rubuta hakan.

 

Ya ce an sake daidaita kasafin kudin tare da hadin gwiwar hukumomin da abin ya shafa, inda sabon jimillar kasafin kudin ya karu zuwa sama da naira biliyan dari da ashirin da uku, ciki wanda kashe kudin yau da kullum ya kai kashi sittin cikin dari, yayin da na ayyukan ci gaba ya tsaya a kashi arba’in cikin dari.

 

Yunusa Shehu Pambegua ya shawarci shugabannin kananan hukumomi da su yi amfani da kasafin kudin yadda ya kamata ta hanyar gudanar da mulki na kowa da kowa don amfanin daukacin al’ummar Jihar Kaduna.

 

‘Yan majalisar sun amince da kudirin ba tare da sabani ba bayan ya tsallake karatu na uku, kuma yanzu ana jiran amincewar gwamna domin ya zama doka.

 

Cov/Shamsudeen Manir Atiku

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Majalisar Dokoki Ta Amince Da Kasafin Kudin

এছাড়াও পড়ুন:

NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi

Kungiyar ‘Yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Kebbi ta raba kayan abinci da kudi ga iyalan mambobinta da suka rasu a lokacin da suke kan aikin jarida, a matsayin kyautar azumin Ramadan.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Kungiyar na Jiha, Kwamared Bello Sarki Abubakar, ya ce suna gudanar da wannan shiri a duk shekara, tun bayan kaddamar da shi da tsohon shugaban kungiyar na jiha Alhaji Aliyu Jajirma ya yi, domin faranta ran iyalan abokan aikinsu da suka rasu.

Kwamared Sarki Abubakar ya bayyana cewa dukkan shugabannin kungiyar da suka gabata sun tabbatar da ci gaba da gudanar da wannan shiri a duk lokacin azumin Ramadan domin rage wa iyalan mamatan radadin wahalhalun rayu.

Ya sanar da cewa kowane iyali daga cikin iyalan mambobi 21 da suka rasu za su karɓi buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 25 da kuma naira dubu goma.

Yayin da yake gode wa Gwamnatin Jihar Kebbi karkashin jagorancin Kwamared Nasiru Idris saboda goyon bayan da take bai wa kungiyar, Kwamared Sarki ya yaba da ayyukan ci gaba da Gwamna Nasir Idris ya aiwatar a cikin shekaru biyu da suka gabata domin inganta rayuwar al’ummar jihar.

Kwamishinan Watsa Labarai da Al’adu na Jihar Kebbi, Alhaji Yakubu Ahmed BK, yayin da yake yaba wa shugabancin kungiyar saboda tallafin da ta bai wa iyalan mamatan, ya tabbatar wa kungiyar cewa Gwamnatin jihar za ta ci gaba da fifita jin daɗin ‘yan jarida a jihar.

Haka kuma, ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa don tabbatar da cewa badi an gudanar da wannan taro cikin gagarumin shiri domin faranta wa iyalan mamatan rai.

A madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, daya daga cikin matan wadanda suka rasu, Hajiya Hadiza Abdullahi, ta gode wa kungiyar saboda tunawa da su bayan rasuwar mazajensu.

 

Daga Abdullahi Tukur

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Wakilai ta janye ƙudirin tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma
  • Majalisar Wakilai ta janye ƙudirin da ke neman tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bada Hutun Sallah Karama Ta 2025/1446
  • Gidauniyar Daily Trust da WRAPA sun ’yanta fursunoni 21 a Kaduna da Katsina
  • Rasha Da Ukraine Sun Amince Da Tsagaita Wuta A Tekun Black Sea
  • Masu neman yi wa Natasha kiranye ba su cika ƙa’ida ba — INEC
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI
  • Ministan Lafiya Ya Yi Alƙawarin Inganta Tallafi Ga Likitoci A Hajjin 2025
  • NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Ƙasa Kiranye