Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ummar Babura Sun Karrama Sabon Shugaban Asibitin Koyarwa Na Rasheed Shekoni

Al’ummar Babura sun shirya gagarumin taron girmamawa domin karrama Dr. Salisu Mu’azu, bayan nada shi a matsayin Daraktan kuma babban likitan asibitin koyarwa na Rasheed Shekoni da ke jihar Jigawa, da kuma samun matsayin mamba na Cibiyar Kasa (mni).

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Kwamitin Shirye-shirye, Rabiu Umar, ya bayyana cewa an gudanar da taron ne domin nuna godiya ga Allah da kuma murnar manyan nasarorin da Dr. Mu’azu ya samu.

Ya yaba da kokarin Daraktan wajen gudanar da aikinsa da kwarewa, da kuma ci gaba da tallafa wa al’umma.

A sakon da aka gabatar a madadin Mai Martaba Sarkin Ringim, Alhaji Dr. Sayyadi Abubakar Mahmoud, wanda Mai Girma Alhaji Usman Sayyadi, Babban Hakimin Masarautar, ya wakilta, ya nuna godiya ga masu shirya taron.

Ya bayyana karramawar a matsayin abin da ya dace da Dr. Mu’azu, yana mai jaddada jajircewarsa, da tausayi da himma wajen yi wa al’umma hidima.

Haka zalika, Shugaban Karamar Hukumar Babura, Alhaji Hamisu Muhammad Garu, ya taya Dr. Mu’azu murna bisa nasarorin da ya samu a fannin aikin likitanci, inda ya danganta hakan da jajircewa da  amana.

Ya tabbatar masa da cikakken goyon bayan al’umma tare da addu’ar samun karin nasarori.

A nasa bangaren, Dr. Salisu Mu’azu ya bayyana godiya sosai bisa girmamawa da karramawar da al’ummarsa ta masa.

Ya kuma nuna godiya ga Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Umar Namadi, bisa damar da ya ba shi zuwa makarantar NIPSS da ke jihar Filato.

A yayin taron, mutane da kungiyoyi daban-daban sun mika kyaututtuka da lambobin yabo ga Daraktan, ciki har da reshen kungiyar likitoci ta Najeriya na jihar Jigawa, J Health Beneficiaries, kungiyar Nas nas da Ungozoma ta kasa, da kuma kungiyar masu kula da lafiyar hakora ta Babura da sauransu.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MDD Ta Nuna Damuwarta Akan Kokarin Sake Raba Kasar Sudan Gida Biyu
  • Zargin Ganduje: Za mu sanar da lokacin yanke hukunci —Kotu
  • EFCC Ta Kama Wasu Mutane 40 Da Ake Zargi Da Yin Damfara Ta Intanet A Neja
  • An taƙaita zirga-zirgar babura da haramta kiwon dare a Filato
  • Gwamnonin Nijeriya Sun Nuna Damuwarsu Kan Kashe-kashen Mutane A Filato 
  • Ina Da Ƙwarewar Da Zan Iya Zama Shugaban Ƙasar Nijeriya – Makinde
  • Gwamnati Ta Ayyana 18 Da 21 Ga Afrilu A Matsayin Hutun Esta
  • UEFA: Barcelona Ta Kai Zagayen Kusa Da Karshe A Karon Farko Cikin Shekaru 9
  • Al’ummar Babura Sun Karrama Sabon Shugaban Asibitin Koyarwa Na Rasheed Shekoni
  • Kokarin Da Iran Take A Tattaunawa Da Amurka Shi Ne Dage Mata Takunkuman Zaluncin Da Aka Dora Mata