Leadership News Hausa:
2025-04-17@09:37:12 GMT

Ministar Wajen Madagascar: Muna Godiya Ga Tawagogin Likitanci Na Sin

Published: 26th, February 2025 GMT

Ministar Wajen Madagascar: Muna Godiya Ga Tawagogin Likitanci Na Sin

Ministar harkokin wajen Madagascar Rasata Rafaravavitafika ta bayyana a Tananarive, hedkwatar kasar jiya Litinin cewa, ana godiya ga Sin da ta dade take tura tawagogin likitanci zuwa kasar cikin shekaru 50 da suka gabata, don ba da tallafin jinya na zamani a yankuna masu nisa na Madagascar, da ceton rayuka na miliyoyin mutane dake wuraren.

Rasata ta bayyana hakan ne yayin halartar bikin sa hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwar tawagogin likitanci ta Sin tsakanin Sin da Madagascar.

Ji Ping, jakadan Sin dake Madagascar da Randriamanantany Zelyarivelo, ministan kiwon lafiyar jama’a na Madagascar, suka sa hannu a kan yarjejeniyar. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rundunar “Gulani” Ta Shiga Sahun Masu Kin Amincewa Da Yaki

A kalla tsoffin sojojin rundunar “Gulani” ta HKI 150 ne su ka rattaba hannu akan takardar yin kira da a dawo da fursunoni gida daga Gaza.

Ita dai rundunar “Gulani” ce mafi karf a tsakanin rudunonin sojan HKI,kuma tun da aka kafa ta, ta shiga dukkanin yake-yaken da HKI ta yi.

Wadanda su ka rattaba hannu akan wasikar sun bayyana goyon bayansu ga wasikar da sojan sama su ka rubuta a ranar 9 ga watan Aprilu da ake ciki,ko da kuwa sakamakon hakan shi ne kawo karshen yaki.

A cikin sa’o’i 48 da su ka gabata,dubban sojojin HKI sun rattaba hannu akan wasika wacce take yin kira da a kawo karshen yakin Gaza da kuma dawo da fursunonin da suke can.

A ranar juma’ar da ta gabata kafafen watsa labaru HKI sun ambaci cewa, da akwai sojojin bayan fage 1000 da su ka rattaba hannu akan wasika, da kuma tsofaffin sojojin soja a tsakaninsu da akwai wadanda suna kan ganiyar aikinsu.

Bayan wannan ne kuma sojojin dake kula da motocin yaki da tankoki su 15,25 su ka bi bayansu, sai kuma wasu tsoffin sojojin sama Jannati ,haka nan kuma sojan ruwa da likitocin soja 100. A cikin kwanaki  kadan da su ka gabata ma dai wasu jami’an daga cikin tsoffin ma’aikatan kungiyar leken asirin soja sun shiga cikin masu rubuta wasikar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  ‘Yan Hamayyar Tanzaniya Sun Ki Amincewa Da Hana Su Shiga Zabe
  • Matashin Da Ya Ƙware Wajen Kashe Mutane Da Ƙwace Ya Miƙa Kansa Ga ‘Yansanda A Kano
  • Za A Watsa Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” Na Harshen Malay
  • Firaministan Malaysia: Xi Jinping Babban Jagora Ne Mai Matukar Mayar Da Hankali Kan Abubuwan Dake Shafar Zaman Rayuwar Jama’a
  • Al’ummar Babura Sun Karrama Sabon Shugaban Asibitin Koyarwa Na Rasheed Shekoni
  • CMG Ta Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Gidan Talabijin Na Kasar Vietnam
  • Mutane 2 Sun Rasu a Wajen Haƙar Ma’adinai A Jihar Neja
  • Rundunar “Gulani” Ta Shiga Sahun Masu Kin Amincewa Da Yaki
  • Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
  • An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” Na Harshen Vietnam