Gwamnatin Neja Ta Haramta Karbar Haraji A Hannun Masu Kananan Sana’o’i
Published: 26th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Neja ta haramta wa masu tattara kudaden shiga a fadin kananan hukumomi ashirin da biyar na jihar karbar haraji daga hannun ‘yan talla da masu kananan sana’o’i.
Gwamnan jihar Mohammed Umar Bago ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a gidan gwamnati Minna, babban birnin jihar.
Mohammed Umar Bago wanda ya yi Allah-wadai da yadda ake karbar kudade ba bisa ka’ida ba a hannun kananan ‘yan kasuwa, ya umurci shugabannin kananan hukumomi da kansiloli da su kara sa ido tare da tabbatar da ganin an kawo karshen irin wadannan ayyuka nan take.
Ya tunatar da su cewa gwamnatin jihar Neja tana da tsarin bai daya da ya hana karbar haraji dafa masu kananan sana’o’i domin basu damar dogaro da kai.
“Mun yanke shawarar cewa daga yanzu, babu wwanimai karamar sana’a da za a sake karbar haraji a hannunsa a wannan jihar.”
“’Yan talla da kananan ‘yan kasuwa ba sa biyan haraji a Jihar Neja, kuma duk wanda aka samu yana karbar haraji daga wurinsu zai dandana kudarsa,” inji Gwamnan.
Daga Aliyu Lawal
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: KASUWANCI karbar haraji
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Yaɗa Labarai Ya Taya Gwamna Bago Murnar Cika Shekara 51
“Jajircewar sa ga haɓaka ababen more rayuwa, noma da ƙarfafa matasa yana ci gaba da mayar da Jihar Neja abin koyi wajen cigaba da wadata.”
Ministan ya ce yana taya gwamnan na jihar su murna, yana mai bayyana shi a matsayin jagora mai kishin hidimta wa al’umma da cigaban ƙasa.
Idris ya ƙara da cewa, “Yayin da yake bikin wannan rana ta musamman, ina taya shi murna a matsayin jagora wanda jajircewar sa ga hidima da shugabanci ke nuna ainihin cigaba.
“Ina roƙon Allah ya ci gaba da ba shi lafiya, hikima da ƙarfi don ya ci gaba da tafiyar da Jihar Neja zuwa matakai mafi girma.”
Ya kammala da taya Gwamna Bago murna, inda ya ce, “A karo na biyu, muna taya ka murna da fatan alheri a wannan rana mai albarka, Mai Girma Gwamna!”