HausaTv:
2025-04-18@07:21:05 GMT

Iyalan Malcolm X sun nemi Trump da ya yi bayani kan makomar batun kisansa

Published: 26th, February 2025 GMT

Iyalan Malcolm X, bakar fata fata kuma daya daga cikin jagororin  musulmin Amurka da aka kashe a ranar 21 ga Fabrairun 1965, sun bukaci shugaban Amurka Donald Trump da ya bayyana bayanan da ke da alaka da kashe shi, kamar yadda shafin Arabi 21 ya ruwaito.

Iyalan Malcolm X sun gabatar da bukatar ne a cikin wata sanarwa da Ben Crump, lauya mai kare hakkin bakar fata a Amurka ya bayar, a wani taro da aka gudanar tare da iyalan Malcolm X a birnin New York na kasar Amurka domin cika shekaru 60 da kashe shi.

Crump, ya yi nuni da wani umarni da Trump ya sanya wa hannu a watan Janairu, inda ya bayyana dukkan bayanan da suka shafi kisan gillar John F. Kennedy, da Martin Luther King, Jr., inda ya bukaci Trump da ya bayyana duk wasu bayanai da suka shafi kisan Malcolm X.

Crump ya bayyana fatansa na cewa Trump zai amsa bukatun iyalan Malcolm X. “Muna sa ran Trump zai dauki mataki a ranar 19 ga Mayu, 2025, a bikin cika shekaru 100 da haihuwar Malcolm X,” in ji shi.

A ranar 19 ga Mayu kowace shekara, Amurkawa da yawa suna bikin “Ranar Malcolm X” don girmama shi a  matsayin daya  daga cikin fitattun masu fafutukar kare hakkin bakar fata a Amurka a cikin shekarun 1960.

Malcolm X ya kasance kwararre wajen Magana da kaifin basira da kuma kwarjini. Amurkawa da dama sun kadu a lokacin da labarin kisansa ya yadu a shekara 1965.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Tana Shirin Mikawa HKI Dubban Boma-Bomai Cikin Makonni Masu Zuwa

Gwamnatin Amurka ta amince da shirin mikawa HKI dubban boma-bomai saboda kashe falasdinawa a Gaza.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa, sojojin HKI suna jiran isowar boma-bomai daga kasar Amurka don fara wani aikin soje na musamman a Gaza. Saboda kawo karshen samuwar Falasdinawa a yankin.

Wata majiyar HKI, yahudawa ta fadawa kamfanin dillancin labaran ‘Ynetnews’ kan cewa sojojin sama na HKI su na dakon isowar boma-bomai har 3000 daga kasar Amurka a cikin yan makonni masu zuwa.

Labarin ya kara da cewa rundunar ta na son ta gudanar da ayyukan soje mai fadin gaske a kan Falasdinwa wanda ya zai kawo karshen Hamas ya kuma kawo karshen samuwar Falasdinawa a yankin.

Labarin ya kara da cewa gwamnatin kasar Amurka ta na shirin aiko da wani karin boma –bomai har 10,000 nan gaba. Yahuda zasu yi amfani da wadannan boma-boman don fadada ayyukansu a yankin, wadanda suka hada da Siriya da Lebanon da kuma ita Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan Najeriya miliyan 150 sun samu ingantacciyar wutar lantarki – Minista
  • Iran Tana Daukan Tattaunawarta Da Amurka Da Muhimmanci Don Neman Warware Takaddamar Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • WTO Ta Yi Gargadi Akan Karin Kudin Fito Na Amurka
  • Majalisa ta gayyaci Kantoman Ribas, Ibok-Ete Ibas
  • Araghchi: babu tattaunawa kan batun tace sinadarin uranium
  • Yadiot Ahranot: Amurka Ta Bayyana Lokacin Ficewarta Daga Syria
  • Amurka Tana Shirin Mikawa HKI Dubban Boma-Bomai Cikin Makonni Masu Zuwa
  • Hamas Ta Fadawa Iyalan Yahudawan Da Take Tsare Dasu A Gaza Kan Cewa ‘Ya’yansu Zasu Koma A Cikin Akwatunan Gawaki
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu ranar Juma’a da Litinin
  • Jagoran Ya Ce: Iran Ba Ta Kallon Tattaunawan Iran Da Amurka A Matsayin Kawo Karshen Takaddama A Tsakaninsu