Iyalan Malcolm X sun nemi Trump da ya yi bayani kan makomar batun kisansa
Published: 26th, February 2025 GMT
Iyalan Malcolm X, bakar fata fata kuma daya daga cikin jagororin musulmin Amurka da aka kashe a ranar 21 ga Fabrairun 1965, sun bukaci shugaban Amurka Donald Trump da ya bayyana bayanan da ke da alaka da kashe shi, kamar yadda shafin Arabi 21 ya ruwaito.
Iyalan Malcolm X sun gabatar da bukatar ne a cikin wata sanarwa da Ben Crump, lauya mai kare hakkin bakar fata a Amurka ya bayar, a wani taro da aka gudanar tare da iyalan Malcolm X a birnin New York na kasar Amurka domin cika shekaru 60 da kashe shi.
Crump, ya yi nuni da wani umarni da Trump ya sanya wa hannu a watan Janairu, inda ya bayyana dukkan bayanan da suka shafi kisan gillar John F. Kennedy, da Martin Luther King, Jr., inda ya bukaci Trump da ya bayyana duk wasu bayanai da suka shafi kisan Malcolm X.
Crump ya bayyana fatansa na cewa Trump zai amsa bukatun iyalan Malcolm X. “Muna sa ran Trump zai dauki mataki a ranar 19 ga Mayu, 2025, a bikin cika shekaru 100 da haihuwar Malcolm X,” in ji shi.
A ranar 19 ga Mayu kowace shekara, Amurkawa da yawa suna bikin “Ranar Malcolm X” don girmama shi a matsayin daya daga cikin fitattun masu fafutukar kare hakkin bakar fata a Amurka a cikin shekarun 1960.
Malcolm X ya kasance kwararre wajen Magana da kaifin basira da kuma kwarjini. Amurkawa da dama sun kadu a lokacin da labarin kisansa ya yadu a shekara 1965.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Manoman tumatir na tafka asara saboda faɗuwar farashi
Yayin da aka fara tsinkar tumatari dan rani a Kano da sauran jihohin da ke samar da tumatar a fadin Nijeriya, rahotanni sun bayyana cewa, farashinsa ya fadi sosai fiye da yadda aka yi zato, lamarin da ya jefa manoman cikin damuwa.
Binciken da Jaridar Aminiya ta gudanar ya nuna cewa, a halin yanzu, ana sayar da kwando daya na tumatir a kan Naira 3,500, yayin da ake sayar da babban kwando a kan Naira 10,000.
40% na matan Kano sun fuskaci cin zarafi a gida —Shugaban Majalisa Dan kwallon Najeriya ya mutu bayan fadowa daga bene a UgandaWani manomin tumatir, Isah Bello Abba ya bayyana cewa, wannan yanayi ya sa manoma cikin fargaba saboda sun kashe kudade masu yawa wajen noman tumatir na rani, amma yanzu suna fuskantar yiwuwar yin babbar asara.
“Mun zuba jari mai yawa a bana, amma daga dukkan alamu, ba za mu samu riba mai yawa ba. Wannan yanayi yana tsoratarwa, kuma muna fatan abubuwa za sudaidaita nan gaba,” in ji shi.
Shugaban Kungiyar Tomato Out Growers Association of Nigeria (TOGAN) reshen Jihar Kano, Alhaji Sani Danladi Yadakwari, ya bayyana cewa, tabbas wannan yanayi abin damuwa ne, musamman ma tunda yanzu ne farkon kakar, ba lokacin kololuwa ba.
Ya ce, kungiyar ta fahimci matsalar kuma tana aiki tare da Gwamnatin Tarayya don ganin an dauki matakan da za su tallafa wa manoman, inda ya tabbatar cewa, nan ba da dadewa ba za a fito da tsarin magance matsalar.
A cewarsa, ɗaya daga cikin hanyoyin magance matsalar ita ce kafa kananan masana’antu na sarrafa tumatir a fadin kasa, wanda zai rage yawan asarar da ake samu yayin girbi da kuma karancin farashi a kasuwa.
Ya yi kira ga masu ruwa da tsaki a bangaren kasuwanci da su fara kafa irin wadannan masana’antu domin bunkasa tattalin arziki da rage radadin da manoma ke fuskanta.