HausaTv:
2025-03-28@14:59:31 GMT

Iyalan Malcolm X sun nemi Trump da ya yi bayani kan makomar batun kisansa

Published: 26th, February 2025 GMT

Iyalan Malcolm X, bakar fata fata kuma daya daga cikin jagororin  musulmin Amurka da aka kashe a ranar 21 ga Fabrairun 1965, sun bukaci shugaban Amurka Donald Trump da ya bayyana bayanan da ke da alaka da kashe shi, kamar yadda shafin Arabi 21 ya ruwaito.

Iyalan Malcolm X sun gabatar da bukatar ne a cikin wata sanarwa da Ben Crump, lauya mai kare hakkin bakar fata a Amurka ya bayar, a wani taro da aka gudanar tare da iyalan Malcolm X a birnin New York na kasar Amurka domin cika shekaru 60 da kashe shi.

Crump, ya yi nuni da wani umarni da Trump ya sanya wa hannu a watan Janairu, inda ya bayyana dukkan bayanan da suka shafi kisan gillar John F. Kennedy, da Martin Luther King, Jr., inda ya bukaci Trump da ya bayyana duk wasu bayanai da suka shafi kisan Malcolm X.

Crump ya bayyana fatansa na cewa Trump zai amsa bukatun iyalan Malcolm X. “Muna sa ran Trump zai dauki mataki a ranar 19 ga Mayu, 2025, a bikin cika shekaru 100 da haihuwar Malcolm X,” in ji shi.

A ranar 19 ga Mayu kowace shekara, Amurkawa da yawa suna bikin “Ranar Malcolm X” don girmama shi a  matsayin daya  daga cikin fitattun masu fafutukar kare hakkin bakar fata a Amurka a cikin shekarun 1960.

Malcolm X ya kasance kwararre wajen Magana da kaifin basira da kuma kwarjini. Amurkawa da dama sun kadu a lokacin da labarin kisansa ya yadu a shekara 1965.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jagora Ya Yi Kira Ga Iraniyawa Su Fito Don Gudanar Da Gagarumar Zanga-Zargar Ranar Kudus Ta Duniya

Imam sayyid Aliyul Khamina’ie Jagoran juyin juya halin musulunci na kasar Iran yayi kira ga mutanen kasar su fito kwansu da kwarkwatansu don halattar zanga-zangar ranar Kududs ta duniya a yau Jumma’a.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jagoran yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar a jiya Alhahamis da yamma. Ya kuma kara da cewa fitowar zanga-zangar ranar Kudus ta duniya alama ce ta hadin kan mutanen kasar Iran, sannan cika alkawali ne ga al-ummar kasar Falasdinu kan cewa mutanen kasar Iran ba zasu taba barinsu su, su kadai ba.

Ranar Qudus ta duniya dai, rana ce wacce Imam Khomaini (q) wanda ya kafa JMI ya ware a ko wace ranar Jumma’a ta karshe na watan Ramadan mai alfarma, na ko wace shekara, don nuna goyon bayan ga al-ummar Falasdinu wadanda ake zalunta, saboda mamayar kasarsu da aka yi. Sannan da kasancewar masallacin Al-Aksa a birnin Qudus al-kiblar musul ce da farko, wanda yake hannun yahudawan sahyoniyya a halin yanzu.

A bana wannan zanga-zangar za’a yi ta ne a dai-dai lokacinda yahudawan suke kissan kiyashi wa falasdinawa a Gaza a karkashin yakin tufanul aksa, wanda ya zuwa yanzu sun kashe falasdiyawa fiye da dubu 50 a yaynsa wasu fiye da dubub 120000 suka ji raunin..

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana Gudanar Da Tarukan Ranar Quds Ta Duniya A Wannan Juma’a
  • Jagora Ya Yi Kira Ga Iraniyawa Su Fito Don Gudanar Da Gagarumar Zanga-Zargar Ranar Kudus Ta Duniya
  • Kasar Sin Na Adawa Da Kara Yawan Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Amurka Ta Takaita Fitar Da Kayayyakinsu
  • MDD ta yi gargadi game da tabarbarewar al’amuran jin kai a Gaza
  • Ranar Kudus: al’ummar Iran zasu nuna hadin kan su ga duniya_ Pezeshkian
  • Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata a matsayin hutun sallaGwamnati Ta Ayyana 31 Ga Maris Da 1 Ga Afrilu A Matsayin Ranakun Hutu Don Bukin Eid-el-Fitr Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hu
  • Gwamnatin Iran Ta Kira Yi Al’ummar Kasar Da Su Fito Domin Halartar Jerin Gwanon Ranar Kudus
  • Duniyarmu A Yau: Ranar Qudus Ta Duniya Ta Shekara 1446
  • Rasha Da Ukraine Sun Amince Da Tsagaita Wuta A Tekun Black Sea
  • Araqchi: Har yanzu Iran ba ta mayar da amsa ga wasikar Trump kan tattaunawar nukiliya ba