HausaTv:
2025-03-28@18:29:24 GMT

Hamas ta yi tir da matakin Isra’ila na shirin takura masu ibada a masallacin Quds

Published: 26th, February 2025 GMT

Kungiyar ​​Hamas ta yi Allah wadai da matakin da Isra’ila ta dauka na sanya takunkumin hana masu ibada shiga masallacin Al-Aqsa a cikin watan Ramadan.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, Hamas ta yi ishara da umarnin da ‘yan sandan Isra’ila suka bayar na ba wa masu ibada 10,000 kawai damar gudanar da sallar Juma’a a harabar masallacin Al-Aqsa, tana  mai cewa matakin wani lamari ne mai matukar  hadari da ke da nufin tauye ‘yancin addini.

Hamas ta ce, umarnin ‘yan sandan Haramtacciyar Kasar Isra’ila  cin zarafi ne  ga dukkan ka’idoji, yarjejeniyoyin da kuma dokoki na kasa da kasa, sannan kuma hakan tsokana ce kai tsaye ga musulmi.

Sanarwar ta kuma jaddada cewa, irin wadannan tsare-tsare ba za su yi tasiri wajen sauya asali da tarihin masallacin Al-Aqsa ba.

Bugu da kari kuma Hamas ta dora alhakin abin da hakan zai iya haifarwa a kan gwamnatin yahudawan sahyuniya masu tsatsauran ra’ayin kin musulunci.

Daga karshe kungiyar Hamas ta yi kira ga kungiyar hadin kan kasashen musulmi da kasashen duniya da su dauki tsauraran matakai domin dakile wannan mataki na keta alfarmar  masallacin Al-Aqsa, da kuma tabbatar da cewa al’ummar Palastinu na gudanar da ibadarsu cikin ‘yanci.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran, Lebanon, Iraki, Yemen sun fara atisayen hadin gwiwa na goyan bayan Gaza

Kasashen Iran, Lebanon, Iraki, da kuma Yemen sun kaddamar da wani atisayen hadin gwiwa na sojojin ruwa domin nuna goyan baya ga  Falasdinawa a zirin Gaza, wadanda ke ci gaba da fuskantar zalinci  na gwamnatin Isra’ila.

An fara faretin hadin gwiwa a tekun Fasha, da yankin gabar tekun Makran, da kuma tekun Caspian da ke arewaci da kuma kudancin yankin ruwan Iran yau Alhamis gabanin ranar Qudus ta duniya.

Kwamandan rundunar sojojin ruwa na IRGC Rear Admiral Alireza Tangsiri ya ce jiragen ruwa masu nauyi da marasa nauyi 3,000 ne ke halartar faretin.

Ya kara da cewa, faretin na da nufin nuna karfin ruwa na bangaren ‘yan gwagwarmaya da kuma isar da sako ga miyagu da azzalumar gwamnatin Isra’ila.

A yayin faretin, an nuna tutar Falasdinu, sannan aka kona tutar Isra’ila a mashigin tekun Farisa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihad Islami: Ranar Quds Dama Ce Ta Hadin Kai Tsakanin Al’umma
  • Ana Gudanar Da Tarukan Ranar Quds Ta Duniya A Wannan Juma’a
  • Kamun Akanta-janar Take-taken Toshe Bakin Gwamnan Bauchi Ne – Ƙungiya
  • Sallah: Yadda ake shirin caɓa ado duk da tsadar kaya
  • Iran, Lebanon, Iraki, Yemen sun fara atisayen hadin gwiwa na goyan bayan Gaza
  • Isra’ila ta sake kashe wani kakakin Hamas
  • Isra’ila : An yi zanga zangar adawa da gwamnatin Netanyahu a Tel-Aviv
  • Za a Fara Cin Moriyar Shirin BEAR III Na UNESCO da Koria Ta Kudu Jihar Kano
  • Ranar Quds : Hamas ta bukaci masu huduba su sadaukar da jawabansu kan Falastinu
  • Wani Bawan Allah Ya Rasu Jim Kadan Bayan Sallar Asuba A Wani Masallaci A Abuja