HausaTv:
2025-02-26@11:43:54 GMT

Hamas ta yi tir da matakin Isra’ila na shirin takura masu ibada a masallacin Quds

Published: 26th, February 2025 GMT

Kungiyar ​​Hamas ta yi Allah wadai da matakin da Isra’ila ta dauka na sanya takunkumin hana masu ibada shiga masallacin Al-Aqsa a cikin watan Ramadan.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, Hamas ta yi ishara da umarnin da ‘yan sandan Isra’ila suka bayar na ba wa masu ibada 10,000 kawai damar gudanar da sallar Juma’a a harabar masallacin Al-Aqsa, tana  mai cewa matakin wani lamari ne mai matukar  hadari da ke da nufin tauye ‘yancin addini.

Hamas ta ce, umarnin ‘yan sandan Haramtacciyar Kasar Isra’ila  cin zarafi ne  ga dukkan ka’idoji, yarjejeniyoyin da kuma dokoki na kasa da kasa, sannan kuma hakan tsokana ce kai tsaye ga musulmi.

Sanarwar ta kuma jaddada cewa, irin wadannan tsare-tsare ba za su yi tasiri wajen sauya asali da tarihin masallacin Al-Aqsa ba.

Bugu da kari kuma Hamas ta dora alhakin abin da hakan zai iya haifarwa a kan gwamnatin yahudawan sahyuniya masu tsatsauran ra’ayin kin musulunci.

Daga karshe kungiyar Hamas ta yi kira ga kungiyar hadin kan kasashen musulmi da kasashen duniya da su dauki tsauraran matakai domin dakile wannan mataki na keta alfarmar  masallacin Al-Aqsa, da kuma tabbatar da cewa al’ummar Palastinu na gudanar da ibadarsu cikin ‘yanci.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar RSF da kawayenta na shirin kafa gwamnatin ‘yan tawaye a Sudan

Kungiyar Rapid Support Forces na Sudan (RSF) sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya tare da kawayenta na kafa gwamnati ta bai daya, a cewar majiyoyin AFP, ba tare da yin la’akari da gargadin da aka yi cewa irin wannan matakin zai raba kasar da yaki ya daidaita ba.

Yarjejeniyar, wacce aka rattaba hannu a kanta a bayan fage a Nairobi babban birnin kasar Kenya, za ta kai ga samar da gwamnatin adawa a kasar Sudan, wadda za ta hada kungiyoyin  Rapid Support Forces, United Civil Forces, da kungiyoyin kwararru, da kuma SPLM-N.

Kamfanin dillancin labaran AFP ya ce, wannan yarjejeniya ta yi kira ga kafa gwamnati mai zaman kanta, da dimokuradiyya, daidaito, da adalci, ba tare da nuna bambanci ga kowane al’adu, kabila, addini, ko yanki ba.

Gwamnatin da aka gabatar na shirin magance gibin ayyuka a yankunan RSF a cewar Alaa El-Din Nuqd, wanda ya jaddada cewa “An katse al’ummar wadannan yankuna daga muhimman ayyuka kamar sabbin takardun kudi da sojoji suka fitar, sarrafa fasfo, da sabunta takardu,” kamar yadda kamfanin dillancin labaran AFP ya nakalto.

Mai magana da yawun rundunar RSF Najm al-Din Drisa ya ce za a iya kafa sabuwar gwamnati nan da wata guda.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugabannin Afirka Ta Kudu, Malaysia Da Colombia Sun Yi Kira Da A Kawo Karshen Laifukan Isra’ila
  • An Cimma Matsaya Kan Sakin Fursunonin Falasdinawa 206 Da Isra’ila Ta Jinkirta
  • Amurka : Kungiyar DAWN Ta Bukaci ICC Ta Binciki Biden Kan Laifin Hada Kai Da Isra’ila A Laifukan Gaza
  • An Bukaci Kafa Dokar Hukuncin Kisa Ga Masu Safarar Da Shan Miyagun Kwayoyi
  • IRGC : Jana’izar Nasrallah Wani Sakon ‘yan Gwagwarmaya A Duniya Baki Daya
  • Kungiyar Hamas Ta Dakatar Da Tattaunawa Da HKI Har Zuwa Sakin Fursinoni Falasdinawa
  • IRGC Ta Bayyana Cewa Taron Jana’izar Nasarallah Ya Yi Tisara A Duniya Gaba Daya Saboda Barazanar Da Jiragen Yakin HKI Ta Yi Wa taron
  • Hamas ta yaba da irin goyon bayan da Sayyed Nasrallah ya baiwa Falasdinu
  • Kungiyar RSF da kawayenta na shirin kafa gwamnatin ‘yan tawaye a Sudan