HausaTv:
2025-04-18@05:24:25 GMT

Shugaban Iran ya sha alwashin inganta hadin gwiwa da Rasha

Published: 26th, February 2025 GMT

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi alkawarin kara bunkasa huldar Iran da Rasha ta hanyar kara  kaimi wajen ga yarjejeniyoyin da ke tsakanin kasashen biyu da kuma ci gaba da mu’amala da cudanya mai ma’ana kan harkokin yankin.

A yayin ganawar da ya yi da ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov da ke ziyara a kasar, Pezeshkian ya bayyana dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da cewa tana kara habaka, tare da jaddada bukatar gaggauta aiwatar da yarjejeniyoyin da ke tsakaninsu, musamman ma cikakkiyar yarjejeniyar hadin gwiwa da ke tsakanin kasashen biyu.

Ya ce, “Iran da Rasha suna da rawar gani da za su iya takawa domin  inganta hadin gwiwarsu, kuma mun kuduri aniyar karfafa huldar dake tsakanin Tehran da Moscow,” in ji shi.

Ya kuma jaddada muhimmancin ci gaba da yin cudanya mai ma’ana a tsakanin kasashen biyu.

Shugaban ya kara da cewa, “Iran da Rasha suna da ra’ayoyi iri-iri kan batutuwan da suka shafi yankin, kuma suna neman karfafa hadin gwiwarsu a matakai na kasa da kasa, ta hanyar huldar dake tsakaninsu, da kuma kungiyoyi irinsu kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai, da kungiyar Eurasia, da BRICS.”

Ministan na Rasha ya kuma jaddada cewa, za a yi duk mai yiwuwa don dorewa da kuma kara habaka wannan hadin gwiwa.

Lavrov ya ce, kammala shigar Iran cikin kungiyar tattalin arzikin Eurasia zai samar da wata sabuwar hanya mai inganci don karfafa dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu – musamman a fannin tattalin arziki da cinikayya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hadin gwiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Zanta Da Tokwaransa Na Kasar Kuwait

A zantawarsa ta wayar tarho da tokwaransa na kasar Kuwait, ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya ce tattaunawarsa da Abdullah Ali Al-Yahya ya fi bada karfi kan al-amuran yankin Asiya ta kudu musamman tattaunawa tsakanin Iran da Amurka kan shirinta na makamshin nukliya da kuma dagewa kasar takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata.

A cikin tattaunawar dai ministan harkokin wajen kasar Kuwai y ace, kasashen yankin da dama sun ji dadin ganin cewa Iran da Amurka suna tattaunawa a tsakaninsu, kuma fatansu shi ne ya zama daga karshe kasashen biyu sun cimma dai-dato don warware matsalolin da ke tsakaninsu ta hanyar tattaunawa.

Aragchi ya bayyana cewa a halin yanzu ba zamu iya fadar menen sakamakon tattaunawar ba, amma da alamun kasashen biyu suna fatan kawo karshen tattaunawar da fahintar juna da kuma cimma yarjeniya mai amfanar bangarorin biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Da Malaysia Za Su Samar Sabbin Shekaru 50 Masu Muhimmanci Na Dangantakar Kasashen Biyu
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Makasudin Rubuta Sakon Jagora Ga Shugaban Kasar Rasha
  • Babban Jami’in Diblomasiyyar Iran Ya Je Birnin Mosco Don Isar Da Sakon Imam Khaminae Ga Putin
  • Majalisar Kasa Ta Rasha Ta Amince Da Yarjeniyar Dangantaka Ta Musamman Tsakanin Iran Da Kasar
  • Sin Da Vietnam Na Fitar Da Sabuwar Taswirar Zamanintar Da Al’Ummunsu Cikin Hadin Gwiwa
  • Rasha ta ce tana bibiyar tattaunawar Iran da Amurka matuka
  • An Watsa Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Masu Jan Hankalin Xi Jinping” A Kasar Malaysia
  • CMG Ta Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Gidan Talabijin Na Kasar Vietnam
  • Xi Ya Isa Kuala Lumpur Domin Ziyarar Aiki A Malaysia
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Zanta Da Tokwaransa Na Kasar Kuwait