HausaTv:
2025-03-28@15:22:33 GMT

Shugaban Iran ya sha alwashin inganta hadin gwiwa da Rasha

Published: 26th, February 2025 GMT

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi alkawarin kara bunkasa huldar Iran da Rasha ta hanyar kara  kaimi wajen ga yarjejeniyoyin da ke tsakanin kasashen biyu da kuma ci gaba da mu’amala da cudanya mai ma’ana kan harkokin yankin.

A yayin ganawar da ya yi da ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov da ke ziyara a kasar, Pezeshkian ya bayyana dangantakar dake tsakanin kasashen biyu da cewa tana kara habaka, tare da jaddada bukatar gaggauta aiwatar da yarjejeniyoyin da ke tsakaninsu, musamman ma cikakkiyar yarjejeniyar hadin gwiwa da ke tsakanin kasashen biyu.

Ya ce, “Iran da Rasha suna da rawar gani da za su iya takawa domin  inganta hadin gwiwarsu, kuma mun kuduri aniyar karfafa huldar dake tsakanin Tehran da Moscow,” in ji shi.

Ya kuma jaddada muhimmancin ci gaba da yin cudanya mai ma’ana a tsakanin kasashen biyu.

Shugaban ya kara da cewa, “Iran da Rasha suna da ra’ayoyi iri-iri kan batutuwan da suka shafi yankin, kuma suna neman karfafa hadin gwiwarsu a matakai na kasa da kasa, ta hanyar huldar dake tsakaninsu, da kuma kungiyoyi irinsu kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai, da kungiyar Eurasia, da BRICS.”

Ministan na Rasha ya kuma jaddada cewa, za a yi duk mai yiwuwa don dorewa da kuma kara habaka wannan hadin gwiwa.

Lavrov ya ce, kammala shigar Iran cikin kungiyar tattalin arzikin Eurasia zai samar da wata sabuwar hanya mai inganci don karfafa dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu – musamman a fannin tattalin arziki da cinikayya.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: hadin gwiwa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa ta janye ƙudirin tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma

Majalisar Wakilai ta janye ƙudurin dokar da ke neman cire rigar kariya ga mataimakin shugaban ƙasa da gwamnoni da mataimakansu.

Hakazalika majalisar ta janye amincewa da ƙudurin da ke neman a soke hukuncin kisa ga masu aikata laifi a ƙasar.

Sallah: Yadda ake shirin caɓa ado duk da tsadar kaya Majalisa ta buƙaci a rage kuɗin data don sauƙaƙa wa ’yan Najeriya 

Ƙudurorin biyu na cikin ƙudurori 42 da suka tsallake karatu na biyu a jiya Laraba.

Shugaban masu rinjaye na majalisar Julius Ihonvbere ne ya gabatar da ƙudurin janyewar.

Mataimakin kakakin majalisar Benjamin Kalu ya ce an ɗauki matakin janyewar ne domin bayar da damar yin muhawara kan ƙudurorin bayan cece-kucen da hakan ya haifar a faɗin ƙasar.

Ƙudurorin na daga cikin gwamman ƙudurorin da majalisar ke nazari a kansu, a wani ɓangare na yin gyaran fuska ga kundin tsarin mulkin ƙasar na shekarar 1999.

Aminiya ta ruwaito cewa, majalisar ta janye ƙudirin ne bayan gwamnatocin jihohin sun bayyana adawarsu kan matakin da ke neman tuɓe musu rigar alfarmar da ke bai wa gwamnoni da mataimakansu da kuma mataimakin shugaban ƙasa kariya daga fuskantar tuhuma kan laifuka.

A ranar Larabar da ta gabata ce ƙudirin ya samu karatu na biyu a zauren majalisar, ƙarkashin jagorancin mataimakin kakakin majalisar, Benjamin Kalu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu zai sake zama shugaban ƙasa a 2027 — Akpabio
  • Jihad Islami: Ranar Quds Dama Ce Ta Hadin Kai Tsakanin Al’umma
  • Najeriya Da Ghana Sun Jaddada Aniyarrsu  Wajen Kara Fadada Alakarsu A Dukkanin Bangarori
  • Kasar Sin Na Adawa Da Kara Yawan Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Amurka Ta Takaita Fitar Da Kayayyakinsu
  • Majalisa ta janye ƙudirin tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma
  •  Kasashen Iran Da Katar Sun Jaddada Muhimmancin Shigar Da Dukkanin Bangarorin  Al’ummar Kasar A Cikin  Sha’anin Kasar
  • Iran, Lebanon, Iraki, Yemen sun fara atisayen hadin gwiwa na goyan bayan Gaza
  • An kama mataimakin shugaban Sudan ta Kudu
  • Ranar Quds : Hamas ta bukaci masu huduba su sadaukar da jawabansu kan Falastinu
  • Ranar Kudus: al’ummar Iran zasu nuna hadin kan su ga duniya_ Pezeshkian