Aminiya:
2025-02-26@12:07:33 GMT

Mayaƙan Boko Haram sun sace kwale-kwale 8 a Borno

Published: 26th, February 2025 GMT

Wasu ’yan ta’adda da ake kyautata zaton mayaƙan Boko Haram ne sun yi fashi da makamin wasu kwale-kwalen kamun kifi guda takwas a hannun masunta a Doron Baga da ke Ƙaramar Hukumar Kukawa ta Jihar Borno.

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Asabar a ƙauyen Kaimo da ke da tazarar kilomita huɗu daga garin Doron Baga.

DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa Mutum 10 sun mutu a hanyar Damaturu zuwa Maiduguri

A cewar wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta, ‘yan ta’addan dauke da muggan makamai da ba a tabbatar da adadinsu ba, sun mamaye ƙauyen inda suka tara masuntan waje guda.

Majiyar ta ce “sun iso ne da makamai, inda suka yi barazanar tayar da hankali idan ba mu bar jiragen ruwanmu ba.”

Ya ƙara da cewa “daga nan ne ‘yan ta’addan suka ƙwace kwale-kwale guda takwas sannan suka tsere ta cikin kogin.

“Muna buƙatar gwamnati ta kawo mana agaji saboda sana’o’in da muke da su a halin yanzu su ne kamun kifi da noma, amma yanzu muna cikin firgici saboda daji ba shi da tsaro.”

A bayan nan dai rahotannin sun tabbatar da cewa ‘yan ta’addar Boko Haram na ci gaba da kafa sansani a gabar tafkin Chadi, musamman a Tumbun Alkali, Tumbun Barebari, Musarram, Shangaram, da Masharam, duk a cikin Ƙaramar Hukumar Kukawa ta Jihar Borno.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram jihar Borno Kwale kwale

এছাড়াও পড়ুন:

IRGC Ta Bayyana Cewa Taron Jana’izar Nasarallah Ya Yi Tisara A Duniya Gaba Daya Saboda Barazanar Da Jiragen Yakin HKI Ta Yi Wa taron

Dakarun kare juyin juya halin musulunci a nan Iran wato IRGC Sun bayyana cewa Jana’zar Sayyid Hassan nasarallah da kuma magajinsa Sayyid Safiyuddeen ya bayyana irin karfin da kungiyar Hizbullah take da shi a kasar da kuma yankin gabas ta tsakiya.

A wani bayani wanda dakarun suka fitar sun bayyana cewa, taron da kungiyar ta gudanar na shahidan shuwagabanninta a jiya, ya tabbatar da cewa kungiyar tana da karfi kuma tana da karfin kawo karshen HKI a yankin da kuma kwato kasashen Larabawan da aka mamaye.

Rahoton ya kara da cewa a fagen kasa da kasa kuma, mutanen da suka taru ko suka yi gangami a jana’izar ya tabbatar da yadda wannan kungiyar take da karbuwa a cikin kasar a kuma kasashen duniya da dama, saboda irin yawan baki daga kasashen waje da suka halarci Jana’izar.

Rahoton ya kara da cewa kokarin da jiragen yakin HKI suka yi na tarwatsa taron a lokacinda ta getta ta kan wurin taron ya nuna karfin wannan kungiyar da kuma yadda mutane suka amince da su. Amma tare da godiyar All..babu wanda ya tanka masu a lokuta biyu da suka ratsa ta kan taron.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙungiya ta rage farashin kayan marmari saboda Azumin Ramadan
  • DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa
  • Sin Ta Nuna Adawa Da Saka Sunayen Kamfanoni Da Wasu Sinawa Cikin Takunkuman EU A Kan Rasha
  • Manoman tumatir na tafka asara saboda faɗuwar farashi
  • Iran A Karon Farko Ta Gwada Aiki Da Sabbin Jiragen Yakin Da Ta Kera A Cikin Atisayen Zulfikar da Ke Gudana A Halin Yanzu
  • IRGC Ta Bayyana Cewa Taron Jana’izar Nasarallah Ya Yi Tisara A Duniya Gaba Daya Saboda Barazanar Da Jiragen Yakin HKI Ta Yi Wa taron
  • Hukumar Tsaro Ta Farin Kaya Ta Kama Wasu Mutane 2 Da Yin Sojan Gona
  • Gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a Borno 
  • ’Yan bindiga sun harbe fasto, sun sace wasu a coci