Aminiya:
2025-04-18@07:23:24 GMT

Mayaƙan Boko Haram sun sace kwale-kwale 8 a Borno

Published: 26th, February 2025 GMT

Wasu ’yan ta’adda da ake kyautata zaton mayaƙan Boko Haram ne sun yi fashi da makamin wasu kwale-kwalen kamun kifi guda takwas a hannun masunta a Doron Baga da ke Ƙaramar Hukumar Kukawa ta Jihar Borno.

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Asabar a ƙauyen Kaimo da ke da tazarar kilomita huɗu daga garin Doron Baga.

DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa Mutum 10 sun mutu a hanyar Damaturu zuwa Maiduguri

A cewar wata majiya da ta nemi a sakaya sunanta, ‘yan ta’addan dauke da muggan makamai da ba a tabbatar da adadinsu ba, sun mamaye ƙauyen inda suka tara masuntan waje guda.

Majiyar ta ce “sun iso ne da makamai, inda suka yi barazanar tayar da hankali idan ba mu bar jiragen ruwanmu ba.”

Ya ƙara da cewa “daga nan ne ‘yan ta’addan suka ƙwace kwale-kwale guda takwas sannan suka tsere ta cikin kogin.

“Muna buƙatar gwamnati ta kawo mana agaji saboda sana’o’in da muke da su a halin yanzu su ne kamun kifi da noma, amma yanzu muna cikin firgici saboda daji ba shi da tsaro.”

A bayan nan dai rahotannin sun tabbatar da cewa ‘yan ta’addar Boko Haram na ci gaba da kafa sansani a gabar tafkin Chadi, musamman a Tumbun Alkali, Tumbun Barebari, Musarram, Shangaram, da Masharam, duk a cikin Ƙaramar Hukumar Kukawa ta Jihar Borno.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram jihar Borno Kwale kwale

এছাড়াও পড়ুন:

An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya

Wasu masu dauke da makamai sun kai hari a wasu kauyuka biyu dake jihar Filato inda su ka kashe mutane 52.

Rahotannin da suke fitowa daga jihar ta Filato sun ambaci cewa wasu makiyaya ne su ka kai  harin na ranar Litinin din da ta gabata an kai shi ne a kan yankin Bassa.

Kamfanin dillancin labarun Reuters da ya dauki labarin ya ambaci cewa,an gano gawawwaki 51 daga cikin wadanda aka kashe din, kuma wani adadi mai yawa na mutanen kauyukan sun jikkata.

Ita kuwa kungiyar “Amnesty International” ta ambaci cewa maharan sun kuma rusa gidaje, tare da wawashe kayan da suke cikinsu. Kungiyar ta zargi jami’an tsaron kasar da gajiyawa wajen tabbatar da tsaro.

Jahar Filato ta dade tana fuskantar fadace-fadace a tsakanin makiyaya da mazauna  kauyuka, duk da cewa daga baya an sami lafawar al’amurran,amma daga baya ya sake dawowa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matan da suka tsira daga Boko Haram na buƙatar tallafin musamman
  • ’Yan bindiga sun sace makiyaya 5, da shanu 1,200 a Kaduna
  • Dangote: Har yanzu gidajen mai ba su rage farashin mai ba
  • An taƙaita zirga-zirgar babura da haramta kiwon dare a Filato
  • Hamas Ta Fadawa Iyalan Yahudawan Da Take Tsare Dasu A Gaza Kan Cewa ‘Ya’yansu Zasu Koma A Cikin Akwatunan Gawaki
  • DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan Riƙo
  • Samarwa Matasa Abun Yi Shi Zai Kawo Ƙarshen Ta’addancin Boko Haram Da ‘Yan Bindiga – Zulum 
  • Lauyoyin London Suna Tattara Bayanai Kan ‘Yan Birtaniya Da Suka Yi  Yaki Cikin Sahun Yahudawan Sahayoniyya A Gaza
  • An Kashe Sojojin Yahudawa A Gaza A Yayinda Wasu Da Dam Suka Ji Rauni
  • An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya