Ahmed Musa ya buƙaci a gudanar da bincike kan mutuwar ɗan wasan Nijeriya a Uganda
Published: 26th, February 2025 GMT
Tauraron tawagar Super Eagles Ahmed Musa ya buƙaci a gudanar da bincike game da mutuwar dan wasa Abubakar Lawal wanda ake zargin ya faɗo daga wani gini ya mutu a kasar Uganda.
A jiya Litinin aka ba da rahoton mutuwar Lawal wanda ‘yan sandan Uganda suka ce ɗan wasan haifaffen Sakkwato ya mutu ne bayan ya faɗo daga benen wani katafaren kanti.
Cikin wani dogon saƙo da Ahmed Musa ya wallafa a shafinsa na X, ya buƙaci a gudanar da cikakken bincike domin tabbatar da gaskiyar lamarin.
“Muna baƙin ciki da samun labarin mutuwar Abubakar Lawal. Wannan lamari ne mai ban tsoro wanda akwai ayar tambayoyi da neman ƙarin haske.
“Saboda mun gano bayanai masu cin karo da juma game da rasuwarsa; Na farko an yi iƙirarin cewa hatsari ne, kuma rahoton na biyu ya ce ya faɗo daga baranda.
“Wadannan rahotannin masu cin karo da juna sun nuna wani abu ne da ke da shakku game da rasuwarsa kuma na tuntubi hukumomin Nijeriya da Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Nijeriya (NFF) su mai da hankalinsu kan wannan mummunan lamari da ya faru a Uganda.
“Ina kira ga gwamnatin Nijeriya da Hukumar NFF da su binciki lamarin, su haɗa kai da gwamnatin Uganda domin a yi wa Lawal adalci.
“Ran Lawal ya cancanci a yi cikakken bincike kuma a yi adalci idan an samu wani da laifi.
“Allah Ya jikansa tare da bai wa iyalansa haƙurin jure wannan babban rashi.”
Haka kuma, sa’o’i bayan faruwar lamarin mai ban takaici, Shugabar Hukumar ’Yan Nijeriya Mazauna Ƙetare (NIDCOM), Abike Dabiri-Erewa ta bayyana cewar akwai “ababen zargi” game da mutuwar Lawal.
“Wannan abin takaici ne kuma kamar akwai rashin gaskiya. Muna buƙatar a gudanar da cikakken bincike. Kada a yi rufa-rufa ko kaɗan.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: a gudanar da
এছাড়াও পড়ুন:
An Gudanar Da Taron Dandalin Ciniki Tsakanin Sin Da Habasha A Addis Ababa
An gudanar da taron dandalin ciniki tsakanin Sin da Habasha kana taron sa kaimi ga dandalin baje kolin tsarin samar da kayayyaki na kasa da kasa wato CISCE karo na 3 a jiya Litinin a Addis Ababa, hedkwatar kasar Habasha.
Kwamitin sa kaimi ga cinikin Sin da ketare da kwamiti mai kula da harkar zuba jari na Habasha da kungiyar kasuwanci da kungiyar sana’o’in Habasha sun gudanar da taro mai taken “Shiga Habasha: Habaka hadin gwiwar tsarin samar da kayayyaki tsakanin Sin da Afirka” cikin hadin kai. Inda wakilai fiye da 200 daga bangarorin gwamnatoci da ciniki da tattalin arziki da kafofin yada labarai da sauransu suka halarci taron.
Jakadan Sin dake Habasha Chen Hai ya gabatar da wani jawabi, inda ya ce, dandalin CISCE irinsa na farko a duniya dake mai da hankali kan tsarin samar da kayayyaki a duniya, zai samar da wani muhimmin dandali ga mabambantan kamfanonin kasashen duniya wajen habaka kasuwaninsu a ketare da jawo jari daga waje da mu’amalar kimiyya da daga kimar kasashensu da dai sauransu.
Darektan kwamiti mai kula da zuba jari na Habasha Zeleke Temesgen ya ce, a halin yanzu, Sin ta zama daya daga cikin abokai mafi karfi a bangaren ciniki da zuba jari ga Habasha. Yana fatan ’yan kasuwan kasar Sin za su nazarci babbar damar zuba jari a kasarsa, da kafa huldar abokantaka mai karfi da dorewa tsakaninsu, a cewarsa. Yana mai fatan shigowar Sin wannan bangare zai gaggauta bunkasa tattalin arzikin kasar, har ma da samar da karin guraben aikin yi da ingiza samun wadata cikin hadin gwiwa baki daya. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp