Ahmed Musa ya buƙaci a gudanar da bincike kan mutuwar ɗan wasan Nijeriya a Uganda
Published: 26th, February 2025 GMT
Tauraron tawagar Super Eagles Ahmed Musa ya buƙaci a gudanar da bincike game da mutuwar dan wasa Abubakar Lawal wanda ake zargin ya faɗo daga wani gini ya mutu a kasar Uganda.
A jiya Litinin aka ba da rahoton mutuwar Lawal wanda ‘yan sandan Uganda suka ce ɗan wasan haifaffen Sakkwato ya mutu ne bayan ya faɗo daga benen wani katafaren kanti.
Cikin wani dogon saƙo da Ahmed Musa ya wallafa a shafinsa na X, ya buƙaci a gudanar da cikakken bincike domin tabbatar da gaskiyar lamarin.
“Muna baƙin ciki da samun labarin mutuwar Abubakar Lawal. Wannan lamari ne mai ban tsoro wanda akwai ayar tambayoyi da neman ƙarin haske.
“Saboda mun gano bayanai masu cin karo da juma game da rasuwarsa; Na farko an yi iƙirarin cewa hatsari ne, kuma rahoton na biyu ya ce ya faɗo daga baranda.
“Wadannan rahotannin masu cin karo da juna sun nuna wani abu ne da ke da shakku game da rasuwarsa kuma na tuntubi hukumomin Nijeriya da Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Nijeriya (NFF) su mai da hankalinsu kan wannan mummunan lamari da ya faru a Uganda.
“Ina kira ga gwamnatin Nijeriya da Hukumar NFF da su binciki lamarin, su haɗa kai da gwamnatin Uganda domin a yi wa Lawal adalci.
“Ran Lawal ya cancanci a yi cikakken bincike kuma a yi adalci idan an samu wani da laifi.
“Allah Ya jikansa tare da bai wa iyalansa haƙurin jure wannan babban rashi.”
Haka kuma, sa’o’i bayan faruwar lamarin mai ban takaici, Shugabar Hukumar ’Yan Nijeriya Mazauna Ƙetare (NIDCOM), Abike Dabiri-Erewa ta bayyana cewar akwai “ababen zargi” game da mutuwar Lawal.
“Wannan abin takaici ne kuma kamar akwai rashin gaskiya. Muna buƙatar a gudanar da cikakken bincike. Kada a yi rufa-rufa ko kaɗan.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: a gudanar da
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Bada Hutun Sallah Karama Ta 2025/1446
Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Litinin 31 ga watan Maris da Talata 1 ga watan Afrilu a matsayin ranakun hutun karamar Sallah.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin cikin gida wadda babbar sakatariyar ma’aikatar Magdalene Ajani ta sanya wa hannu.
A cikin sanarwar, ministan harkokin cikin gida na Najeriya Olubunmi Tunji-Ojo ya buƙaci dukkanin Musulmai su rungumi tausayawa da karamci da zaman lafiya, inda ya jaddada muhimmancin nuna soyayya da yafiya da haɗin kai domin gina alumma mai cike da zaman lafiya.
Ya kuma buƙaci alummar Musulmi su yi wa Najeriya addu’ar ɗorewar zaman lafiya da samun ci gaba, kuma ya yi kiran gudanar da bukukuwan sallah lafiya.