Aminiya:
2025-02-26@14:01:53 GMT

Sanata Natasha na neman diyyar N100bn wurin Akpabio

Published: 26th, February 2025 GMT

Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya a Majalisar Dattawa, Natasha Akpoti-Uduaghan ta shigar da ƙara a kotu tana ƙalubalantar shugaban majalisar, Godswil Akpabio, kan zargin ɓata mata suna.

Natasha ta shigar da ƙarar ne gaban Babbar Kotun Tarayya a ranar Talata, tana mai ƙarar Akpabio da babban mai taimaka masa Mfon Patrick.

Mutum 10 sun mutu a hanyar Damaturu zuwa Maiduguri Babu hannun Naira Marley a mutuwar Mohbad — Kotu

Ta nemi Kotun Tarayyar da ta umarci waɗanda ake karar su biya ta diyyar naira biliyan 100 kan zargin ɓata mata suna, sannan a biya ta naira miliyan 300 a matsayin kuɗin shigar da ƙara.

Akpoti, wadda lauyanta Victor Giwa ya shigar da ƙarar a madadinta, ya yi ƙorafi kan kalaman da babban mai taimaka wa Shugaban Majalisar Dattawan ya wallafa a shafinsa na Facebook.

Ta nemi kotun ta tilasta wa mutanen janye kalaman, sannan su nemi afuwarta a wani shafin jarida.

Ta ɗora zargin nata ne kan wani saƙo da ta ce Mista Patrick ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda ya soke ta cewa “ba ta san komai ba game da zaman majalisa…da kuma saka tufafi masu shara-shara.”

Barista Giwa ya yi zargin cewar kalaman ba komai ba ne illa, ɓata suna, da takalar faɗa, da ƙanskantar da ita a idon abokan aikinta, da sauran al’umma.

Sanata Natasha ta buƙaci kotun da ta haramta wa waɗanda ake ƙara ko makusantansa daga wallafa duk wani rubutu na ɓatanci a game da ita.

A makon da ya gabata ne Sanata Natasha Akpoti Uduaghan ta bayyana damuwa kan yadda aka bai wa wani ɗan majalisa wurin zamanta, saboda wasu sauye-sauye da aka yi a tsarin zaman majalisar.

Sanatar ta ƙi amincewa da sauyin wajen zaman da aka yi mata, wanda hakan ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin ta da Akpabio.

Lamarin na zuwa ne yayin da aka umarci kwamitin ladabtarwa na Majalisar Dattawan da ya gayyaci Sanata Natasha don bin bahasi kan rikicin sauyin wajen zaman.

A bayan nan ne aka yi zazzafar musayar yawu tsakanin Sanata Natasha da Akpabio kan sauya mata wurin zaman da ta ce an yi ba tare da amincewarta ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: diyya

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙungiya ta raba wa marayu da mabuƙata kayan makaranta a Kano

Ƙungiyar Youths for Progressive Union (YUO), ta raba wa yara marayu da masu ƙaramin ƙarfi a unguwar Kofar Mata da ke Jihar Kano, kayayyakin makaranta.

Kayayyakin sun haɗa da littattafai, alƙalami, jakunkuna, da sauran kayan koyo don taimaka wa yaran da iyayensu suka rasu ko kuma ba su da ƙarfi.

Shugabannin APC sun gana gabanin babban taron jam’iyyar na ƙasa Kamfanin Saudiyya ya haɗa kai da gwamnatin Jigawa kan noman dabino

Sakataren ƙungiyar, Kwamared Usman Bello Kofar Mata, ya ce sun bayar da taimakon ne, domin rage yawan yara da ke gararamba a tituna, musamman marayu.

“Mun ga yadda wasu yara ke shiga tsaka mai wuya bayan rasuwar iyayensu.

“Wasu ba su da kowa da zai kula da su, sai dai su riƙa yawo kamar awaki. Don haka, muka yi bincike muka zaƙulo irin waɗannan yara don mu taimaka musu,” in ji shi.

Taron rabon kayayyakin ya samu halartar mai unguwar Kofar Mata, Alhaji Muhammad Jibril, wanda ya yi kira da a riƙa taimakon marayu da mabuƙata domin hana lalacewar tarbiyyar yara a yankin.

Ya ce rashin irin wannan taimako ne ke janyo koma-baya a yankin Arewa, inda ya bayar da misali da Kudancin Najeriya inda ake ɗaukar nauyin marayu har su girma su zama mutane nagari a rayuwa.

“Idan har ba a taimaka wa marayu da mabuƙata ba, za su tashi babu tarbiyya.

“Idan yaro ba shi da gata, babu wanda zai gyara masa hanya. Amma idan ana tallafa masa, zai girma da sanin darajar rayuwa,” in ji shi.

Ya buƙaci iyaye da al’umma su ci gaba da kula da tarbiyyar yara tare da basu kulawa da taimako domin su zama mutane nagari da za su amfanar da al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙungiya ta raba wa marayu da mabuƙata kayan makaranta a Kano
  • Nebenzia : Hare-haren Sojojin Isra’ila a Lebanon da Syria na kara dagula lamura a yankin
  • Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
  • Iran : Makaman Kare Dangi Na Israila Barazana Ne Ga Zaman Lafiya Da Tsaro
  • Matar Gwamnan Kebbi Ta Rarba Tallafin Kayan Noma Ga Mata Manoma 100 
  • Da Ɗumi-ɗumi: NNPP Ta Dakatar Da Sanata Kawu Sumaila Da Wasu ‘Yan Majalisa Uku
  • Wakilin Jagoran Juyi A Wurin Jana’izar Sayyid: Gwgawarmaya Za Ta Ci Gaba
  • Babu ɗan Arewa mai hankali da zai yi tallan APC a 2027 – Jigo a PDP
  • Gwamnatin Katsina Ta Kashe Naira Biliyan 5.7 Wajen Sayen Awaki 40,000 Domin Raba Wa Mata