Amurka : Kungiyar DAWN Ta Bukaci ICC Ta Binciki Biden Kan Laifin Hada Kai Da Isra’ila A Laifukan Gaza
Published: 26th, February 2025 GMT
Kungiyar kare hakkin bil’adama ta DAWN mai hedkwata a birnin Washington ta yi kira ga kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ICC da ta binciki rawar da tsohon shugaban Amurka Joe Biden da wasu jami’an Amurka suka taka wajen taimakawa Isra’ila ta aikata laifukan yaki a Gaza.
A bukatar da aka mika wa mai gabatar da kara na kotun ICC Karim Khan a ranar 19 ga watan Janairu, 2025, wacce ta bayyana a ranar Litinin, kungiyar mai zaman kanta ta Democracy Now for the Arab World (DAWN) ta zargi Biden, sakataren harkokin wajen Amurka, Antony Blinken, da sakatarensa na tsaro, Lloyd Austin, da taimakawa Isra’ila ta aikata laifukan yaki a Gaza.
A cewar kungiyar mai zaman kan ta, ana kuma zarginsu da bada gudummuwarsu da gangan wajen aikata wadannan laifuka.
Takardar ta nuna goyon bayan gwamnatin Biden na soja, siyasa ga laifukan Isra’ila, wadanda suka hada da jigilar makamai da suka kai dala biliyan 17.9 tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023, musayar bayanan sirri da kariyar diflomasiyya, kamar kin amincewa da kudurin tsagaita wuta da yawa a Majalisar Dinkin Duniya da Kwamitin Tsaro.
“Akwai kwararan dalilai na bincikar Joe Biden, Antony Blinken da Lloyd Austin saboda hadin kai a cikin laifukan Isra’ila,” in ji mamban kwamitin DAWN Reed Brody a cikin wata sanarwa, yana mai cewa: “Bama-baman da aka jefa kan asibitocin Falasdinu, makarantu da gidajensu, na Amurka ne, kuma an gudanar da yakin da kisa da zalunci tare da taimakon Amurka. »
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci Al’umma Da Su Rika Taimakawa Hukumomin Tsaro Da Muhimman Bayanai
Gwamnatin Tarayya ta yi kira ga ‘yan Najeriya da su rika ba da muhimman bayanai ga hukumomin tsaron kasar nan.
Ministan tsaro, Alhaji Badaru Abubakar ne ya yi wannan kiran a lokacin da yake jawabi a wani taron jama’a na gwamnatin jihar Jigawa da aka gudanar a karamar hukumar Birnin Kudu.
A cewar sa, kiran ya zama wajibi domin karfafa tsaro a fadin Najeriya.
Alhaji Badaru Abubakar, ya yi nuni da cewa an samu ingantuwar harkokin tsaro a fadin kasar cikin ‘yan watannin nan.
Ya kuma bayyana cewa, gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu ta yi iya bakin kokarinta wajen yaki da rashin tsaro, kuma za ta ci gaba da jajircewa wajen cimma manufofin da ake so.
Ministan ya yi nuni da cewa, gwamnatin tarayya za ta ci gaba da bayar da duk wani tallafi ga sojojin Najeriya da ke fagen fama don tabbatar da an maido da tsaro.
Badaru Abubakar wanda shi ne tsohon gwamnan jihar Jigawa, ya bayyana jin dadinsa da yadda ya mika ragamar shugabanci ga gwamnati mai inganci.
Ya yabawa gwamnatin Gwamna Umar Namadi bisa gagarumin ayyukan raya kasa da aka gudanar a jihar cikin shekara daya da rabi.
“Na yi farin cikin ganin manyan ayyukan raya kasa da wannan gwamnati ta aiwatar, a cikin shekara daya da rabi da ta wuce,” in ji Ministan.
Gidan rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, wasu daga cikin manyan baki da suka halarci bikin sun hada da, mataimakin gwamnan jihar, Injiniya Aminu Usman, da tsohon gwamnan jihar Barista Ali Sa’ad Birnin Kudu, da sakataren gwamnatin jihar Malam Bala Ibrahim, da sarakuna da malaman addinai, da manyan jami’an gwamnati da dai sauransu.
Usman Muhammad Zaria.