An Cimma Matsaya Kan Sakin Fursunonin Falasdinawa 206 Da Isra’ila Ta Jinkirta
Published: 26th, February 2025 GMT
An cimma matsaya tsakanin Isra’ila da Hamas kan sakin fursunomin Falasdianwan nan 206 da Isra’ila ta jinkira, bayan da Hamas ta saki ‘yan Isra’ila shida.
An dai tsara sakin fursunonin a ranar Asabar data gabata, saidai Isra’ila ta jinkirta sakin falasdinawan bisa abinda ta kira rashin gamsuwa da cin wulakanta ‘yan kasarta gabanin sakin da kungiyar Hamas ke yi.
Bayanai sun ce za’a saki falasdinawan su 206 a cikin sa’o’I 24 masu zuwa.
Dangane da dakatar da sakin fursunonin, Hamas ta zargi Isra’ila da “saka dukkan yarjejeniyar tsagaita wuta a cikin hatsari mai tsanani” tare da yin kira ga kasashe masu shiga tsakani da su shiga tsakani.
A nata bangaren, Hamas za ta mika wasu gawawwakin ‘yan Isra’ila hudu da ta yi garkuwa da su.
Kuma za a yi hakan ne ba tare da wani biki ba, ba tare da shirya taron da kungiyar Hamas ta saba yi ba wajen sallamar wadanda ta yi garkuwa dasu.
Za a mika gawarwakin ne tare da kungiyar agaji ta Red Cross, amma kuma da taimakon Masar.
A cewar sojojin Isra’ila, daga cikin mutane 251 da aka yi garkuwa da su a ranar 7 ga Oktoba, 62 suka rage a Gaza, sannan 35 daga cikinsu sun mutu.
A ranar 1 ga watan Maris mai shirin kamawa ne ya kamata matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wutar ta tsakanin Isra’ila da Hamas ta kawo karshe, domin shiga mataki na biyu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu ranar Juma’a da Litinin
Gwamnatin Tarayya ta ayyana Juma’a, 18, da kuma Litinin, 21 ga watan Afrilun 2025 a matsayin ranakun hutun bikin Easter a faɗin ƙasar.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Talata.
Barcelona da PSG sun tsallaka zagayen kusa da na ƙarshe a Gasar Zakarun Turai DAGA LARABA: Dalilan Ɓaraka A Tsakanin Iyayen Riƙo Da Ƴaƴan RiƙoA jawabin da Babbar Sakatariya a Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida , Dokta Magdalene Ajani ta fitar, Ministan ya nemi mabiya addinin Kirista su yi amfani da wannan lokaci wajen yi wa ƙasar addu’o’in zaman lafiya da haɗin kai.
Yayin da yake taya mabiya addinin Kirista murnar wannan lokaci, Mista Tunji yana kuma kira ga al’ummar Nijeriya da su haɗa hannu da gwamnatin Shugaba Bola Tinubu a ƙoƙarin da take yi na inganta rayuwar al’umma ta hanyar ci gaban ƙasa.