HausaTv:
2025-02-26@15:22:02 GMT

Araghchi : Iran Ba Za Ta Shiga Tattaunawa Da Amurka Bisa Matsin Lamba

Published: 26th, February 2025 GMT

Iran ta bayyana cewa ba zata shiga wata tattaunawa da Amurka ba kan shirinta na nukiliya bisa matsin lamba.

Ministan harkokin wajen Iran ne Abbas Araghchi ya bayyana hakan, inda yake cewa muddin fadar White House ba ta janye matsin lamba wa kasar ba, babu wata tattaunawa.

“A kan tattaunawar nukiliya, matsayin Iran a bayyane yake: ba za mu yi shawarwari cikin matsin lamba, barazana, da takunkumi ba.

“Saboda haka,” in ji ministan harkokin wajen Iran, “babu yuwuwar yin shawarwari kai tsaye tsakaninmu da Amurka kan batun nukiliya matukar dai ana ci gaba da yin amfani da mafi girman matsin lamba a yadda take a halin yanzu.”

Misra Araghchi ya bayyana hakan ne a yayin  wani taron manema labarai da takwaransa na Rasha, Sergey Lavrov da ke ziyara a Tehran.

Ministan harkokin wajen kasar ya ce Iran za ta magance batun nukiliyar tare da hadin gwiwa da kawayenta – Rasha da China.

A nasa bangare da yake bayyani game da shirin nukiliyar Iran, Lavrov ya ba da fifiko kan hanyar diflomasiyya.

“Mun yi imanin cewa har yanzu akwai karfin diplomasiyya don warware batun nukiliyar Iran, kuma muna fatan za a iya samun mafita. Ba Iran ce ta haifar da wannan rikicin ba.” Inji shi.

Iran dai ta dade tana fuskantar takunkumin da kasashen yamma suka kakaba mata kan ayyukanta na nukiliya, da batun kare hakkin bil’adama, da dai sauransu, saidai zuwan Donald Trump, ya kara dagula al’amuran inda ya sha alwashin matsin lamba kan kasar ta Iran, domin ta mika wuya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka : Kungiyar DAWN Ta Bukaci ICC Ta Binciki Biden Kan Laifin Hada Kai Da Isra’ila A Laifukan Gaza

Kungiyar kare hakkin bil’adama ta DAWN mai hedkwata a birnin Washington ta yi kira ga kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ICC da ta binciki rawar da tsohon shugaban Amurka Joe Biden da wasu jami’an Amurka suka taka wajen taimakawa Isra’ila ta aikata laifukan yaki a Gaza.

A bukatar da aka mika wa mai gabatar da kara na kotun ICC Karim Khan a ranar 19 ga watan Janairu, 2025, wacce ta bayyana a ranar Litinin, kungiyar mai zaman kanta ta Democracy Now for the Arab World (DAWN) ta zargi Biden, sakataren harkokin wajen Amurka, Antony Blinken, da sakatarensa na tsaro, Lloyd Austin, da taimakawa Isra’ila ta aikata laifukan yaki a Gaza.

A cewar kungiyar mai zaman kan ta, ana kuma zarginsu da bada gudummuwarsu da gangan wajen aikata wadannan laifuka.

Takardar ta nuna goyon bayan gwamnatin Biden na soja, siyasa ga laifukan Isra’ila, wadanda suka hada da jigilar makamai da suka kai dala biliyan 17.9 tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023, musayar bayanan sirri da kariyar diflomasiyya, kamar kin amincewa da kudurin tsagaita wuta da yawa a Majalisar Dinkin Duniya da Kwamitin Tsaro.

“Akwai kwararan dalilai na bincikar Joe Biden, Antony Blinken da Lloyd Austin saboda hadin kai a cikin laifukan Isra’ila,” in ji mamban kwamitin DAWN Reed Brody a cikin wata sanarwa, yana mai cewa: “Bama-baman da aka jefa kan asibitocin Falasdinu, makarantu da gidajensu, na Amurka ne, kuma an gudanar da yakin da kisa da zalunci tare da taimakon Amurka. »

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka : Kungiyar DAWN Ta Bukaci ICC Ta Binciki Biden Kan Laifin Hada Kai Da Isra’ila A Laifukan Gaza
  • Messi Zai Fuskanci Hukunci A Gasar MLS Ta Kasar Amurka
  • Iyalan Malcolm X sun nemi Trump da ya yi bayani kan makomar batun kisansa
  • Amurka Za Ta Illata Kanta Bisa Tsara Matakan Kayyade Samar Wa Sin Sassan Na’urorin Laturoni Na Semiconductor
  •  Fizishkiyan: Ba Za Mu Zauna Kan Teburin Tattaunawa Da Wanda Yake  Yi Mana Barazana Ba
  • Iran : Makaman Kare Dangi Na Israila Barazana Ne Ga Zaman Lafiya Da Tsaro
  • Araghchi : Bai Kamata A Rika Murgude Hakkin Dan Adam Ana Shishigi A Harkokin Cikin Gidan Kasashe Ba
  • Amurka Ta Laftawa Iran Wasu Sabbin Takunkumai
  • Amurka Ta Zama Jagorar Bata Ka’idoji Da Dokar Duniya Bisa Amfani Da Makamin Harajin Kwastam