HausaTv:
2025-03-28@19:24:09 GMT

                          Me Turkiya Take So A Syria?

Published: 26th, February 2025 GMT

 A farko-farkon da masu dauke da makamai su ka kwace iko da birnin Halab, jami’an gwganatin Turkiya sun kaucewa yin Magana akan abinda yake faruwa.

Sa dai kuma da yake mai kaza a aljihu ba ya jimirin cas, ba a je ko’ina ba, su ka fara furta kalaman da suke nuni da cewa, Da kawai rina a kaba. Ministan harkokin wajen Turkiya Hakan Fidan, ya yi tsokaci akan abinda yake faruwa a Syria, ya zargi  tsohuwar gwamnatin Syria da cewa; Ba ta yi aiki da bangarorin yarjejeniyar Astana ba.

Sojojin Turkiya suna cikinm kasar Syria tun a farkon 2018, inda suke mamaye da kaso 10% na yankin wannan kasa. Kuma aiki a tare da masu adawa da gwamnatin Damascuss,musamman rundunar da ake kira da             “ Sojojin Kasar Syria” wacce aka kafa  a cikin garin Orfa a ranar 4 ga watan Oktoba na shekarar 2019. Kafa wannan rundunar ya kasance kwanaki kadan gabanin hasken da Amurka da Rasha su ka bai wa Turkiyan ta kai wa Kurdawa hari a gabashin tekun Euphrates.

 Turkiya din ce take bai wa wannan runudnar makami da kudi da albashi da dukkanin abinda suke bukata domin maye gurbin rundunar “ Free Syrian Army” wacce ita ma a cikin kasar Turkiya aka kafa ta a  watan Ogusta na 2011.

 Kafafen watsa labarun Turkiya suna kaucewa ambaton rawar da gwamnatin kasar tasu take takawa a cikin abubuwan da suke faruwa a cikin Syria. Abinda suke cewa shi ne: “ Rundunar ‘yan adawa ta Syria”, ko kuma su kira su da “ Masu adawa da Assad.” Haka nan kuma suna kiransu da |Rundunar Hatsh” ba tare da sun fayyace abinda wadannan haruffan  hudu suke nufi ba da kuma alakarta da rundunar; Jubhatun-Nusrah’. Wannan kungiyar kuwa sunanta ta ‘yan ta’adda a bisa dokar da shugaban Turkiya Urdugan ya rattabawa hannu a ranar 29 ga watan Ogusta na 2018.

Kafafen watsa labarun gwamnati na Turkiya ba su Magana akan alakar da take a tsakanin rundunar  Jaisuhl Watani al-Suri”da kuma |Hay’atult-tahirish-sham.” da suke a cikin garin Idlib, kuma Turkiyan ce ta rika ba su dukkanin abubuwan da suke bukatuwa da su na man fetur, wutar lantarki, ruwa, internet, da dukkanin hajar da ake amfani da ita ta yau da kullum. Tsakanin iyakar Turkiya zuwa Idlib, kilo  mita 40 ne kadai.Bugu da kari ana kashe kudaden Turkiya a cikin wannan yankin na Idlib. Haka nan kuma babu wata hanyar da za iya shiga cikinsa sai ta hanyar Turkiya, wato dai a fakaice za a iya cewa, an yanke wanann yankin da Syria ya zama wani bangare na Turkiya.

Bayan wannan, kafafen watsa labarun na Turkiya sun rika Magana akan muhimmancin  da garin Halab yake da shi a wurin Turkiya, ko da kuwa na wucin gadi ne. Hakan ta faru ne bayan da rundunar “Jaishul Watani al-Suri” ya kwace iko da garin Tal-Rif’ da kuma korar  mayakan Kurdawa daga cikinsa, haka nan wasu unguwanni a cikin birnin na Halab.

Kurduwan dai sun shimfida ikonsu ne a cikin wadannan yankunan bisa yarjejeniya da  tsohuwar gwamnatin Damascuss.

Kafafen watsa labarun na Turkiya sun rika bayyana abinda ya faru da cewa, bugu ne mai kyau da aka yi wa Kurdawa da kawo musu cikas, a kokarin da suke yin a kafa yankinsu mai cin gashin kansa a cikin Syria. Haka nan kuma kafafen watsa labarun ta Turkiya sun rika yi wa Kurdawan barazana cewa sojoji za su mamaye gabashin tekun “Eupherate” da can ne cibiyar kurdawan idan an gama da ‘yantar da dukkanin Syria da kifar da gwamnatin Asad.

 Bugu da kari, kafafen watsa labarun Turkiyan sun rufe idanunsu akan yadda  daruruwan masu dauke da makamai da su ka shiga cikin birnin Halab, suke Magana da harshen turkanci da Karin harshe irin an Uzabakistan, Shishan, da Kuma Egoz na kasar China.

 **

Wani abu da ya fi bayar da mamaki shi ne yadda wasu Turkawa, su ka fara cewa, ai dama gundumar Halab, ta turkiya ce, domin tana a karkashin Daular Usmaniyya har zuwa 1918, an kuma kori Turkawa daga ciki ne bayan da aka yi galaba akan Daular Usmaniyya a yakin duniya na farko.

Wannan labarin na Turkiya, ya yi kama da abinda Turkawan su ka rika fada a lokacin abinda aka kira da “Yunkurin Larabawa” a 2011 da su ka rika yin bore a cikin kasashe mabanbanta domin samun ‘yanci. A wancan lokacin Turkawan sun rika cewa, yankunan Halab, Idlib, Riqqah, Deir-zur, da kuma arewacin Iraki wato Mausel,  Karkuk da Arbil da Sulaimaniyya, duk wani yanki ne na Turkiya. Wasu kuma sun rika cewa, Idlib ce jahar Turkiya ta 81.

 Bugu da kari an rika ganin hotuna da tutocin Turkiya akan ginin “Wani tsohon gini mai tarihi na garin Halab.

A ranar Talata 10 /12/2024 shugaban kungiyar kishin turkancin “Daulat Bahshali “ya bayyana cewa” Halab Gari ne na Turkawa.”

Loakcin da ‘yan tawayen masu dauke da makamai suke shirin shiga garin Halab, Turkiya ta umarce su da kar su cutar da mazaunasa domin ba ta damar aiwatar da shirinta na tattalin arziki wanda ya kunshi, ba su wutar lantarki, man fetur da dukkanin hajojin da suke da bukatuwa da su. Wanann shi ne abinda Turkiyan ta tsara a tsawon shekaru 13 na yaki.

Ankara ta so ganin cewa duk inda  ‘yan tawaye su ka shiga su yi kyakkyawar mu’amala da mutane, saboda ita kuma ta ci moriyar hakan ta fuskar tattalin ariziki.

A karshe kuwa, mayakan sun shiga birnin Damscuss, inda su ka zama gwaraza, sannan kuma Turkiya ta zama wata gwarzuwa da kuma a nan gaba za ta ci moriyar taimakawa ‘yan adawa na shekaru masu tsawo, ta fuskokin siyasa da tattalin arziki.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

WFP: Yara Miliyan 11 Na Fama Da Karanci Abinci A Nijeriya

Wani sabon rahoto da hukumar samar da abinci ta duniya (WFP) ta fitar a Nijeriya, na ishara da cewa mutum miliyan 11 ne a fadin jihohi shida na Arewa maso Gabas da Arewa maso Yammacin Nijeriya ke fuskantar matsalar karancin abinci a shekarar 2025.

Kazalika, rahoton ya danganta matsalar da rashin tsaro da ake ci gaba da fuskanta, da hauhawar farashin kayan abinci da man fetur, da bala’in yanayi, da kuma matsugunan jama’a, ya sa miliyoyin mutane ke fafutukar samun abinci mai gina jiki.

Rahoton UNICEF ya kara bayyana cewa yara ‘yan kasa da shekaru biyar a Nijeriya, kusan miliyan 11, na fama da matsanancin rashin abinci, wanda hakan ya sa kashi 50 cikin 100 na ka fuskantar barazana ga rayuwarsu.

Rahoton ya bayyana rashin wadataccen abinci mai gina jiki, da wahalhalun tattalin arziki na iya zama ummul-haba’isin muhimman abubuwan da ke haifar da rashin abinci ga yara.

A cikin 2024 kadai, kungiyar (MSF) ta ce ta yi wa yara sama da 300,000 maganin tamowa, doriyar kashi 25 cikin 100 daga 2023.

Daga cikin wadannan kaso, 75,000 na bukatar kulawar rashin lafiya mai tsanani, yayin da 250,000 aka basu kulawa ta hanyar shirye-shiryen sama musu lafiya a fadin jihohi bakwai: Borno, Bauchi, Katsina, Kano, Sokoto, Zamfara, da Kebbi.

Wakilin kungiyar ta MSF na kasa Dr Simba Tirima ya shaida wa LEADERSHIP cewa kungiyar agajin ta lura da yadda ake samun karuwar masu dauke da cutar, wanda ya zarce shekarun baya a duk cibiyoyin kula da lafiyarsu.

“Rashin abinci mai gina jiki na kara ta’azzara, tare da samun karin yara a wuraren da ake kula da su,” in ji Dr Tirima.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba
  • A Cikin Mako Daya An Yi Asarar Naira Biliyan 365 A Kasuwar Sayar Da Hannun Jari
  • Jihad Islami: Ranar Quds Dama Ce Ta Hadin Kai Tsakanin Al’umma
  • WFP: Yara Miliyan 11 Na Fama Da Karanci Abinci A Nijeriya
  • Kamun Akanta-janar Take-taken Toshe Bakin Gwamnan Bauchi Ne – Ƙungiya
  •  Kasashen Iran Da Katar Sun Jaddada Muhimmancin Shigar Da Dukkanin Bangarorin  Al’ummar Kasar A Cikin  Sha’anin Kasar
  • MDD ta yi gargadi game da tabarbarewar al’amuran jin kai a Gaza
  • An kama mataimakin shugaban Sudan ta Kudu
  •  Sojojin Sudan Sun Kwace Wuri Na Karshe Da Yake A Hannun “Rundunar Kai Daukin Gaggawa” A Cikin Birnin Khartum
  • DAGA LARABA: Yadda Farashin Kayan Masarufi Suke Gabanin Sallah