Aminiya:
2025-03-29@01:01:14 GMT

Shugabannin APC sun gana gabanin babban taron jam’iyyar na ƙasa

Published: 26th, February 2025 GMT

Shugabannin Jam’iyyar APC, ciki har da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, gwamnoni, da sauran manyan jagorori, sun gana a daren Talata a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

An gudanar da taron ne domin shirye-shiryen babban taron jam’iyyar na ƙasa da za a yi a yau a hedikwatar APC.

Kamfanin Saudiyya ya haɗa kai da gwamnatin Jigawa kan noman dabino Sanata Natasha na neman diyyar N100bn wurin Akpabio

Wannan shi ne taron farko da za a yi taron tun bayan hawan Shugaba Tinubu kan mulki a ranar 29 ga watan Mayu, 2023.

A bara, an tsara shirya waɗannan taruka ne a watan Satumba, amma aka ɗage su ba tare da saka sabuwar rana ba.

A baya-bayan nan, tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya soki shugabannin jam’iyyar da rashin shirya taruka, inda ya ce APC ta fara rabuwa da aƙidun da aka gina ta a kai.

An fara taron ne da misalin ƙarfe 7:30 na dare, bayan isowar Shugaba Tinubu.

Batutuwan da aka tattauna sun haɗa da shirin gudanar da babban taron jam’iyyar, matsalolin shari’a da ke shafar jam’iyyar, cibiyar nazari da tsara manufofin APC da sauransu.

Waɗanda suka halarci taron sun haɗa da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, Kakakin Majalisar Wakilai Tajudeen Abbas, Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje.

Sauran sun haɗa da wasu gwamnoni kamar Hope Uzodinma (Imo), Babajide Sanwo-Olu (Legas), Dapo Abiodun (Ogun), da Babagana Umar Zulum (Borno).

Haka kuma, mambobin kwamitin jam’iyyar da tsohon shugaban APC na ƙasa, Cif Bisi Akande, sun halarci taron.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa

Wasu mutane huɗu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne sun mutu a sakamakon hatsarin mota a Jihar Nasarawa.

Kakakin rundunar ‘yan sanda jihar SP Nansel Rahman, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa, inda ya ce lamarin ya auku ne lokacin da ‘yan fashin ke ƙoƙarin tserewa jami’an.

Gidauniyar Zakkah ta raba wa marayu 100 kayan sallah a Gombe Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati

“A ranar 25 ga watan Maris ne rundunarmu ta samu wani kiran gaggawa kan wasu ‘yan fashi na tsaka da ta’asa a bayan filin wasa na ƙaramar hukumar Keffi.

“Bayan samun kiran ne kwamishinan ‘yan sanda Shettima Jauro Mohammed ya ba da umarnin bin bayan ‘yan fashin nan take.

“Suna cikin guje mana ne a cikin motar da suka sace ƙirar Toyota Camry suka yi haɗari a babban titin Abuja-Keffi.

“Jami’anmu da ke ofishin ‘yan sanda na Goshen ne suka kwashe su zuwa asibiti, a nan mutum huɗu suka mutu.

“Ɗayan da ya rage kuma na hannunmu likitoci na bashi kulawa.

Binciken ‘yan sanda dai ya kai ga gano wasu kayan da ‘yan fashin suka sata da suka haɗa wayoyin hannu 12, agogunan hannu, sai makamai da suka haɗa da manyan wuƙaƙe biyu, sukundireba, da kuma layu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban CMG Ya Gana Da Ministar Raya Al’adu Ta Rasha
  • Girgizar ƙasa ta kashe mutum 150 a Myanmar da Thailand
  • Tinubu zai sake zama shugaban ƙasa a 2027 — Akpabio
  • Sallah: Hadimin gwamnan Sakkwato ya bai wa magoya bayan APC kyautar N22m
  • Majalisa ta janye ƙudirin tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma
  • Majalisar Wakilai ta janye ƙudirin tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma
  • Majalisar Wakilai ta janye ƙudirin da ke neman tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma
  • Wang Yi Ya Gana Da Mataimakin Shugaban Kwamitin Kasa Na Amurka Mai Lura Da Alakar Sin Da Amurka
  • Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4
  • ’Yan fashi 4 sun mutu yayin tsere wa ’yan sanda a Nasarawa