Shugabannin APC sun gana gabanin babban taron jam’iyyar na ƙasa
Published: 26th, February 2025 GMT
Shugabannin Jam’iyyar APC, ciki har da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, gwamnoni, da sauran manyan jagorori, sun gana a daren Talata a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.
An gudanar da taron ne domin shirye-shiryen babban taron jam’iyyar na ƙasa da za a yi a yau a hedikwatar APC.
Kamfanin Saudiyya ya haɗa kai da gwamnatin Jigawa kan noman dabino Sanata Natasha na neman diyyar N100bn wurin AkpabioWannan shi ne taron farko da za a yi taron tun bayan hawan Shugaba Tinubu kan mulki a ranar 29 ga watan Mayu, 2023.
A bara, an tsara shirya waɗannan taruka ne a watan Satumba, amma aka ɗage su ba tare da saka sabuwar rana ba.
A baya-bayan nan, tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya soki shugabannin jam’iyyar da rashin shirya taruka, inda ya ce APC ta fara rabuwa da aƙidun da aka gina ta a kai.
An fara taron ne da misalin ƙarfe 7:30 na dare, bayan isowar Shugaba Tinubu.
Batutuwan da aka tattauna sun haɗa da shirin gudanar da babban taron jam’iyyar, matsalolin shari’a da ke shafar jam’iyyar, cibiyar nazari da tsara manufofin APC da sauransu.
Waɗanda suka halarci taron sun haɗa da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, Kakakin Majalisar Wakilai Tajudeen Abbas, Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje.
Sauran sun haɗa da wasu gwamnoni kamar Hope Uzodinma (Imo), Babajide Sanwo-Olu (Legas), Dapo Abiodun (Ogun), da Babagana Umar Zulum (Borno).
Haka kuma, mambobin kwamitin jam’iyyar da tsohon shugaban APC na ƙasa, Cif Bisi Akande, sun halarci taron.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
IRGC : Jana’izar Nasrallah Wani Sakon ‘yan Gwagwarmaya A Duniya Baki Daya
Rundinar kare juyin juya halin musulinci ta Iran, ta bayyana bikin jana’izar sakataren kungiyar Hezbollah ta Lebanon mai rasuwa Sayyed Hassan Nasrallah da kuma Sayyed Safiedinne da aka gudanar a matsayin wani babban sako na ‘yan gwagwarmaya ga duniya baki daya.
Wannan babban taron da akayi a Beirut abun tarihi ne ga duniyar musulmi, ya kuma nuna cewa kungiyar Hizbullah, na da karfinta da kuma akidar kyamar sahyoniyawan.
Sanarwar ta kara da cewa: “Bikin da ya samu halartar miliyoyin mutane, a daidai lokacin da ake barazana da jiragen yakin Isra’ila, ya zama wata alama ta karfin Musulunci da cikakken hadin kan al’ummar kasar Labanon.
Sanarwar ta yi nuni da cewa, gagarumin taron makoki daga kasashe daban-daban, addinai da kabilu, da jam’iyyun siyasa, sun sabunta mubaya’a ga shahidan ‘yan gwagwarmayar, tare da bayar da martani mai karfi ga makiya.