Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da sama da Naira Biliyan Biyar domin biyan diyya ga wadanda aikin gina tituna a cikin  gari ya shafa.

Kwamishinan yada labarai da matasa da wasanni da al’adu na jiha Alhaji Sagir Musa Ahmed ya bayyana hakan ga manema labarai bayan taron majalisar zartarwa ta jiha da aka gudanar a gidan gwamnati da ke Dutse.

A cewarsa, aikin titin ya shafi garuruwa musamman Fagam, da Kila da Jugwa, da Sakuwa, da Gwaram, da Sankara, da Ringim da Bulangu, da Kafin Hausa, da Gandun Sarki, da Hadejia, da Dansure, da Roni, da Aujara, da Jahun da kuma karamar hukumar Dutse, kamar yadda ma’aikatar filaye, da gidaje, da raya birane da tsare-tsare na yanki suka gabatar.

Ya ce, majalisar ta kuma amince da kashe sama da naira biliyan takwas da miliyan dari biyu a matsayin kashi 30 bisa  na kudaden shirin noman rani na shinkafa na shekarar 2025.

Ya kuma yi bayanin cewa, an  amince da hakan  ne da nufin samar da wadataccen abinci da inganta rayuwar miliyoyin al’ummar  Jigawa ta hanyar bai wa Manoma 58,500 rance, don noma hekta 50,000 na shinkafa a fadin yankunan da ake noman shinkafa,  kamar yadda ma’aikatar noma da albarkatun kasa ta gabatar.

Kwamishinan ya ce, majalisar zartaswa ta jihar ta kuma amince da sanya hannu kan yarjejeniyar tsawaita wa’adin shekaru 2 tsakanin ma’aikatar lafiya ta gwamnatin jihar Jigawa da kungiya mai zaman kanta ta Medicins San Frontiers (MSF)  da ke kasar Faransa.

A cewarsa, rattaba hannu kan yarjejeniyar na da nufin karfafa kokarin jihar na rage mace-macen mata masu juna biyu da jarirai, ta hanyar samar da ingantacciyar kula ga masu juna biyu a babban asibitin Jahun da kuma cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko na Miga da Ajura.

 

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Diya Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Za a Fara Cin Moriyar Shirin BEAR III Na UNESCO da Koria Ta Kudu Jihar Kano

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana kudirinta na tallafawa shirin inganta ilimi na bunkasa Afirka (BEAR) III, wani shiri na hadin gwiwa da hukumar kula da ilimi da kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya (UNESCO) da Jamhuriyar Koriya suka yi.

 

A wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan wayar da kan jama’a ma’aikatar ilimi ta jihar Kano Balarabe Abdullahi Kiru, yace aikin yana da nufin haɓaka ilimin fasaha da na sana’a a faɗin Afirka, tare da mai da hankali kan ƙarfafa tsarin ilimin fasaha da na sana’a da horo (TVET).

 

Aikin zai mayar da hankali ne kan harkar noma, tare da mai da hankali kan sarrafa kayan noma da sarrafa su bayan girbi.

 

 

A cewar Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dakta Ali Haruna Abubakar Makoda, shirin na BEAR III ya yi daidai da ajandar Gwamna Abba Kabir Yusuf na inganta shirye-shiryen koyon sana’o’i don dogaro da kai.

 

Ya kuma ba da tabbacin cewa gwamnatin jihar Kano za ta ci gaba da hada gwiwa da hukumar UNESCO da kasar Koriya ta Kudu domin bunkasa koyar da sana’o’i a makarantun furamare da na gaba da sakandare a fadin jihar.

 

 

Darakta a ma’aikatar ilimi ta tarayya Dr. (Mrs) M.A Olodo ta jagoranci wata tawaga zuwa jihar Kano domin gudanar da taro da masu ruwa da tsaki dangane da aiwatar da shirin na BEAR III.

 

Ta ba da tabbacin cewa ƙungiyar za ta yi amfani da mafi kyawun lokacin da ya rage don cimma manufofin aikin.

 

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, an gina aikin na BEAR III akan ginshikai guda uku: sanya aikin ya dace da bukatun kasashe masu cin gajiyar shirin, da inganta TVET da ake bayarwa, da kuma kyautata fahimtarsa ​​a tsakanin matasa.

 

Za a gudanar da aikin a kasashe hudu na yammacin Afirka: Najeriya, Ghana, Cote d’Ivoire, da Saliyo.

 

Rel/ Khadijah Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Adadin mamata a girgizar kasar Myanmar ya ka 1,644
  • Wadanda Iftila’in Tankar Mai Ya Sha A Jigawa Sun Sami Naira Miliyan 4 Kowannensu
  • A Cikin Mako Daya An Yi Asarar Naira Biliyan 365 A Kasuwar Sayar Da Hannun Jari
  • Gwamnatin Amurka Tana Shirin Dakatar Da Bada Kudaden Tallafi Don Samar Da Wasu Magunguna
  • Karfin Lantarki Da Tashoshi Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Ke Samarwa A Sin Ya Kai Kilowatt Biliyan 2
  • Majalisar Wakilai ta janye ƙudirin tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma
  • Majalisar Wakilai ta janye ƙudirin da ke neman tuɓe wa matakaimakin shugaban ƙasa da gwamnoni rigar alfarma
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bada Hutun Sallah Karama Ta 2025/1446
  • Za a Fara Cin Moriyar Shirin BEAR III Na UNESCO da Koria Ta Kudu Jihar Kano
  • Kantoman Ribas ya dakatar da hadiman Fubara