Gwamnatin Jigawa Za Ta Biya Diyar Sama Da Naira Biliyan 5 Ga Wadanda Aikin Tituna Ya Shafa
Published: 26th, February 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da sama da Naira Biliyan Biyar domin biyan diyya ga wadanda aikin gina tituna a cikin gari ya shafa.
Kwamishinan yada labarai da matasa da wasanni da al’adu na jiha Alhaji Sagir Musa Ahmed ya bayyana hakan ga manema labarai bayan taron majalisar zartarwa ta jiha da aka gudanar a gidan gwamnati da ke Dutse.
A cewarsa, aikin titin ya shafi garuruwa musamman Fagam, da Kila da Jugwa, da Sakuwa, da Gwaram, da Sankara, da Ringim da Bulangu, da Kafin Hausa, da Gandun Sarki, da Hadejia, da Dansure, da Roni, da Aujara, da Jahun da kuma karamar hukumar Dutse, kamar yadda ma’aikatar filaye, da gidaje, da raya birane da tsare-tsare na yanki suka gabatar.
Ya ce, majalisar ta kuma amince da kashe sama da naira biliyan takwas da miliyan dari biyu a matsayin kashi 30 bisa na kudaden shirin noman rani na shinkafa na shekarar 2025.
Ya kuma yi bayanin cewa, an amince da hakan ne da nufin samar da wadataccen abinci da inganta rayuwar miliyoyin al’ummar Jigawa ta hanyar bai wa Manoma 58,500 rance, don noma hekta 50,000 na shinkafa a fadin yankunan da ake noman shinkafa, kamar yadda ma’aikatar noma da albarkatun kasa ta gabatar.
Kwamishinan ya ce, majalisar zartaswa ta jihar ta kuma amince da sanya hannu kan yarjejeniyar tsawaita wa’adin shekaru 2 tsakanin ma’aikatar lafiya ta gwamnatin jihar Jigawa da kungiya mai zaman kanta ta Medicins San Frontiers (MSF) da ke kasar Faransa.
A cewarsa, rattaba hannu kan yarjejeniyar na da nufin karfafa kokarin jihar na rage mace-macen mata masu juna biyu da jarirai, ta hanyar samar da ingantacciyar kula ga masu juna biyu a babban asibitin Jahun da kuma cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko na Miga da Ajura.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
An Yi Kira Ga Jihohi Da Su Kara Samar Da Ingantacciyar Hanyar Kiyon Lafiya
An bukaci gwamnatocin jihohi da su kara samar da tsarin kula da kiwon lafiya na bai daya (UHC) ga ‘yan kasa domin tabbatar da samar da ingantaccen kiwon lafiya a kasar.
Jami’ar Ayyuka, Kula da Lafiya ta Duniya ga Mata a Lafiya ta Duniya, Najeriya (WGH), Dokta Sienne Oluwatosin Orogun, ta yi wannan kiran a wani taro mai taken “Amfani da Dabaru da Tsarin Gida don Haɓaka Tsarin Kiwon Lafiyar Duniya” a Ilorin, jihar Kwara.
A cewarta akwai tsare-tsare da aka tsara don samar da inshorar lafiya mai araha ga masu rauni a cikin al’umma, ta kara da cewa aiwatar da ingantaccen aiki ya kasance kalubale.
Tun da farko a nata jawabin, kwamishiniyar lafiya ta jihar Kwara, Dokta Amina El-Imam, ta jaddada cewa hukumar kula da lafiya ta duniya (UHC) ita ce manufar tabbatar da cewa dukkan mutane sun samu cikakkiyar kulawar kiwon lafiya da suke bukata ba tare da fuskantar matsalar kudi ba.
Dokta El-Imam ya nuna damuwarsa kan kalubale kamar matsalolin kudade da karancin ma’aikata.
Ta ci gaba da cewa gwamnatin jihar na kokarin ganin an cimma kashi 15 cikin 100 na kasafin kudin jihar a fannin kiwon lafiya, da inganta iya aiki da kuma rike hannun mafi kyawu a cikin bukatun duniya.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU