Ƙungiya ta raba wa marayu da mabuƙata kayan makaranta a Kano
Published: 26th, February 2025 GMT
Ƙungiyar Youths for Progressive Union (YUO), ta raba wa yara marayu da masu ƙaramin ƙarfi a unguwar Kofar Mata da ke Jihar Kano, kayayyakin makaranta.
Kayayyakin sun haɗa da littattafai, alƙalami, jakunkuna, da sauran kayan koyo don taimaka wa yaran da iyayensu suka rasu ko kuma ba su da ƙarfi.
Shugabannin APC sun gana gabanin babban taron jam’iyyar na ƙasa Kamfanin Saudiyya ya haɗa kai da gwamnatin Jigawa kan noman dabinoSakataren ƙungiyar, Kwamared Usman Bello Kofar Mata, ya ce sun bayar da taimakon ne, domin rage yawan yara da ke gararamba a tituna, musamman marayu.
“Mun ga yadda wasu yara ke shiga tsaka mai wuya bayan rasuwar iyayensu.
“Wasu ba su da kowa da zai kula da su, sai dai su riƙa yawo kamar awaki. Don haka, muka yi bincike muka zaƙulo irin waɗannan yara don mu taimaka musu,” in ji shi.
Taron rabon kayayyakin ya samu halartar mai unguwar Kofar Mata, Alhaji Muhammad Jibril, wanda ya yi kira da a riƙa taimakon marayu da mabuƙata domin hana lalacewar tarbiyyar yara a yankin.
Ya ce rashin irin wannan taimako ne ke janyo koma-baya a yankin Arewa, inda ya bayar da misali da Kudancin Najeriya inda ake ɗaukar nauyin marayu har su girma su zama mutane nagari a rayuwa.
“Idan har ba a taimaka wa marayu da mabuƙata ba, za su tashi babu tarbiyya.
“Idan yaro ba shi da gata, babu wanda zai gyara masa hanya. Amma idan ana tallafa masa, zai girma da sanin darajar rayuwa,” in ji shi.
Ya buƙaci iyaye da al’umma su ci gaba da kula da tarbiyyar yara tare da basu kulawa da taimako domin su zama mutane nagari da za su amfanar da al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kayayyakin Makaranta Kofar Mata Ƙungiya Marayu
এছাড়াও পড়ুন:
Luwadi: Magijanci ya lalata dan shekara 5 a Zariya
Mutanen unguwa sun kama wani magidanci mai shekara 45 kan zargin sa da lalata wani yaro ɗan makarantar firamare ta hanyar luwadi a yankin Zariya ta Jihar Kaduna.
Al’ummar yankin sun ce dama ana zargin mutumin da yi wa yara maza fyade, don haka suke ta bibiyar motsinsa, kuma yaron ya faɗa da bakinsa cewa kusan sau uku mutmin yana ɗaukar sa.
Wanda ke zargin yana sana’ar sayar da rake ne a Bakin Dago Tudun Jukun a Karamar Hukumar Zariya Jihar Kaduna.
Aminiya ta ziyarci xibiyar da ke kula da cin zarafin mata da ƙananan yara da ke Asibitin Gambo Sawaba Kofar Gayan Zariya domin samun sahihin bayani kan lamarin a likitance.
Magidanci ya sari matarsa da adda har lahira Ya daɓa wa yayansa wuƙa saboda Naira 700 Luwaɗi: An yanke wa ɗalibai biyu hukuncin bulala a bainar jama’aManajar Cibiyar, Hajiya A’isha Ahmed ta ce a ranar 12 ga watan 2 2025 ofishin ’yan sanda da ke Gonar Ganye, gundumar Tukur Tukur ya kawo wani yaro ɗan shekara 5 kuma ɗan aji ɗaya a makarantar firamare da ake zargin mutumin da lalatawa.
Bayan likitoci sun duba sun gano cewa yaron duburarsa ta bude, wanda hakan ke nuni da an yi yunƙurin zakke masa ta duburarsa.
Hajiya A’isha Ahmed ta ce sun dora yaron a kan magani har na tsawon kwanaki 28 kuma za su rika bibiyar sa domin su tabbatar da cewa yana amfani da maganin yadda ya kamata.
Ta ci gaba da cewa za ta tura sakamakon zuwa ga Kwamishinan Lafiya na Jihar Kaduna, kuma ta tabbatar da cewa sun bai wa jami’an ’yan sanda kwafin binciken.
Hajiya A’isha Ahmed ta yi kira ga iyaye da su daina boye irin wannan mugun abin da ke faruwa da yaransu wai don gudun abin kunya ko halin da yaran za su shiga.
Ta kara da cewa zuwa asibitin da yaran da aka ci zarafinsu a kan lokaci yana taimakawa wajen kula da lafiyarsu.
Mahaifin yaron da aka ɓata ya koka kan yadda ya ce wasu makusantan wanda ake zargin suke ƙoƙarin ɗanne shi da kuma kare shi wanda ake zargin.
Ya ce “abin mamaki shi ne ta yadda suka bi ta hannun mai anguwa wai a bani kuɗi na bar maganar,” DOn haka ya ce a shirye yake da ya bi haƙƙin ɗan nasa domin daƙile irin hakan a nan gaba ga ’ya’yan wasu.
Duk ƙoƙarin jin ta bakin mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ASP Mansur Hassan, ya ci tura, domin layin wayarsa ta ƙi shiga, kuma har rubutaccen sakon da aka aika masa bai amsa ba.