Aminiya:
2025-03-29@09:42:47 GMT

Buhari da El-Rufai ba su halarci babban taron APC ba

Published: 26th, February 2025 GMT

Jam’iyyar APC mai mulki, ta gudanar da babban taronta na ƙasa a Abuja, wanda ya samu halartar manyan jiga-jigan jam’iyyar daban-daban.

Duk da kasancewar Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima a waje taron, wasu manyan shugabannin jam’iyyar ba su halarci taron ba.

Ƙungiya ta raba wa marayu da mabuƙata kayan makaranta a Kano Shugabannin APC sun gana gabanin babban taron jam’iyyar na ƙasa

Daga cikin waɗanda ba su halarci taron ba akwai tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, tsohon gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, da tsohon gwamnan Ribas, Rotimi Amaechi.

Dalilin Rashin Halartar Buhari

Dangane da dalilin da ya sa Buhari bai samu halartar taron ba, tsohon mai magana da yawunsa, Malam Garba Shehu, ya bayyana cewa tsohon shugaban bai samu katin gayyata a kan lokaci ba.

“Taron masu ruwa da tsaki ne, wanda ya kamata Buhari ya halarta. Amma an aike masa da gayyatar taron ne a ranar Litinin, sai dai bai samu wasiƙar ba sai ranar Talata da rana.

“A wannan lokacin, ba zai iya barin Daura ya tafi Abuja don halarta ba, ko da kuwa yana da jirginsa na musamman.”

Duk da hakan, Garba Shehu ya jaddada cewa Buhari har yanzu cikakken ɗan jam’iyyar APC ne kuma zuciyarsa tana tare da ita.

Dalilin Rashin Halartar El-Rufai da Amaechi

Babu cikakken bayani game da dalilin da ya sa Malam Nasir El-Rufai bai halarci taron ba.

Sai dai a baya, tsohon gwamnan na Kaduna ya sha bayyana rashin jin daɗinsa game da jagorancin jam’iyyar, inda zargi cewa ta sauka daga aƙidar da aka kafa ta.

Duk da haka, ya nanata cewar har yanzu shi cikakken ɗan jam’iyyar.

Shi ma Rotimi Amaechi bai bayyana dalilin rashin halartarsa ba.

A kwanakin baya dai, tsohon gwamnan na Ribas ya daina yawan magana a fili.

A wata hira da ya yi da BBC, ya ce: “Idan akwai abu guda ɗaya da na koya daga Shugaba Buhari, shi ne rage yawan surutu.

“Domin ya taba fada min cewa ‘Amaechi, ba don abinci kawai aka yi ciki ba.’“

Manyan Jiga-Jigan da Suka Halarci Taron

Daga cikin gwamnonin da suka halarci taron akwai na jihohin Edo, Benuwe, Ondo, Ekiti, Kaduna, Jigawa, Nasarawa, Yobe, Nejs, Legas, Kogi, Ogun, da Imo.

Mataimakin gwamnan Ebonyi da wasu tsofaffin gwamnoni daga Kogi, Kebbi, Neja, Zamfara, da Filato su ma sun halarci taron.

Duk da rashin halartar wasu daga cikin manyan jiga-jigan jam’iyyar, babban taron ya gudana kamar yadda aka tsara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buhari jam iyya taro tsohon gwamnan halarci taron babban taron

এছাড়াও পড়ুন:

Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID

Kungiyar bada agajin ta gaggauwa ta “white Helmets” na kungiyar Al’kaida, wacce kuma take samun tallafin gwamnatin Amurka ta hukumar USAID ta rasa tallafin da take don gudanar da ayyukanta.

Kamfanin dillancin labaran Spunik na kasar Rasha ya bayyana cewa, kasashen yamma musamman Amurka sun yi amfani da kungiyar ta Al-qaeda a lokacin yakin kasar Syriya a shekara ta 2011 zuwa 2017 don ingiza kasashen yamma kan gwamnatin kasar Siriya na cewa ta yi amfani da makaman guba a kan mutane, don cimmmai manufofinsu a kasar ta Siriya.

A halin yanzu dai shugaban Trump zai dakatar da tallafin da ya ke bawa kungiyar mai yuwa saboda sun cimma manufarko a kasar Siriya ta kifar da gwamnatin Bashar a Al’asad. A kalla mutane kimani 40 daga cikin kungiyar ne suka tabbatar da cewa a lokacin yakin sun kai hare kan sojojin Bashar Al-asad, sannan sun yi amfani da wani yaro dan sheakara 5 Omran don farfaganda kan gwamnaton Bashar Al-Asad, kamar yadda mahaifinsa ya fallasa daga baya.

Kasashen Amurka Burtania da Nethalanda duk sun taimakawa kungiyar da miliyoyin dalar Amurka don gudanar da ayyukansu. Amma a bana shugaba Trump ya yanked alar Amurka miliyon 30 da aka warewa kungiyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar “White Helmets Ta” A Kasar Siriya Ta Rasha Tallafin Da Take Samu Daga USAID
  • MDD Ta Yi Gargadi Akan Mummunan Yanayin A Sudan Ta Kudu
  • Ƙungiyar JNI ta raba wa marayu 50 kayan Sallah a Borno
  • Taron Boao Ya Sake Ba Duniya Damar Ganin Abubuwa Masu Jan Hankali Game Da Sin
  • Tinubu zai sake zama shugaban ƙasa a 2027 — Akpabio
  • Sallah: Hadimin gwamnan Sakkwato ya bai wa magoya bayan APC kyautar N22m
  • Ina Fatan Ci Gaba Da Kasancewa A Manchester United – Onana
  • NLC a Zamfara sun Bada Wa’adin Kwanaki 14 a Aiwatar da Mafi Karancin Albashi
  • Tsohon hadimin gwamnan Kano, Abdullahi Tanka Galadanci, ya rasu
  • Hukumar IAEA ta yi ishara da yiwuwar sake komawa teburin tattaunawa tare da Iran