Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno
Published: 26th, February 2025 GMT
’Yan Ta’addan Boko Haram sun kai hari ƙauyen Kaleri da ke Ƙaramar Hukumar Jere a Jihar Borno, inda suka sace mutum biyu da kayan abinci masu tarin yawa.
Wata majiya daga yankin ta tabbatar da cewa lamarin ya faru ne kusa d Jami’ar Maiduguri (UNIMAID).
Buhari da El-Rufai ba su halarci babban taron APC ba Ƙungiya ta raba wa marayu da mabuƙata kayan makaranta a KanoMajiyar ta ce, “Sun shigo da manyan makamai, suna harbe-harbe suna bi gida-gida don neman kayan abinci, suna sanya tsoro a zukatan mazauna garin.
Wani mazaunin yankin da ya nemi a sakaya sunansa ya ce, “Sun yi garkuwa da mutane biyu, sannan suka kwashe kayan abinci.”
Bayan faruwar lamarin, jami’an ’yan sanda sun rufe yankin tare da kama wasu mutane, amma ba su bayyana cewar waɗanda suka kama na da alaƙa da harin ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram Garkuwa Kayan abinci Ƙauye kayan abinci
এছাড়াও পড়ুন:
Ina Mafita Game Da Ƙalubalen Ƙarancin Abinci A Nijeriya
Jihohin da wannan matsalar ta fi shafa sun hada da, Zamfara, Borno, Yobe da kuma Katsina, musamman duba da yadda aukuwar yawan rikice-rikice, ya tarwatsa rayuwar miliyoyin alumomin yakin da fadawa cikin kangin fatara da yunwa da kuma rashin samun wadataccen abinci.
A ra’ayin mu, matsalar karancin abinci a kasar nan, ba voyayayen abu bane, musammamn duba da cewa, yawan aukuwar tashe-tashen hankula, kalubalen rashin tsaro da matsatin tattalin arziki, suna manyan hummulhaba’isin da ke janyo karancin abinci a a cikin alumma.
Misali, yawan samun hare-haren ‘yan bindiga a yankin kudu maso gabas, ayyukan ‘yan bindiga daji a yankin arewa masu yamma da kuma rikice-rikicen kabilanci a sauran yankuanan, sun janyo tarwatsa miliyoyin alumomi daga matsugunan su, lalata gonakansu wanda hakan ya janyo, aka samu raguwar noma amfanin gona, sauyar da amfanin gonar, inda hakan ya kuma haifar da karancin abinci a cikin alumma tare da samun hauhawan farashin kayan abinci.
Akasarin fannin noma a kasar nan, ya dogara ne kachokam kan samun ruwan damina, inda kuma fanin ke cin karo da samun sauyin yanayi, wanda hakan ke sanya wa a fusaknaci fari ko sauyin samun yanayin saukar ruwan sama da kuma akuwar annobar ambaliyar ruwan sama, inda hakan ke yiwa amfanin gona da aka shuka illa da kuma shafar dabbobi.
Wannan matsalar ta ambaliyar ruwansaman ba wai ta tsaya a kan amfanin gona bane, ta na kuma lalata matsunan alumma da kuma kara haifar da talauci a tsakanin su.
Sauye-sauye na dogon zango kan tattalin arziki da Gwamnatin Tarayya mai ci ta kirkiro da su a shekarar 2024 ta kuma wanzar da su, sun kasance za su iya janyo nakasu, a yunkurin da ake yi na samar da wadataccen abinci a kasar nan.
Duba da yadda ake ci gaba da samun hauhawan farashin kaya, karyewar darajar Naira, samun karuwar farashin man fetur, hakan yakara haifar da tsadar noma amfanin gona, tsadar sufuri, wanda hakan zai kara sanya wa masu sayen kayan abincin, su saya da tsadar gaske.
Bugu da kari, matsain na tattalin arzikin ya kuma janyowa alumma rashin samun wasu abubuwa kamar na iya kula da kiwon lafiyarsu da ci gaba da daukar nauyin karatun ‘ya’yansu.
Hukumar FOA tare da sauran masu ruwa da tsaki da suka hada da sasshen samar da abinci na Majalisar dinkin Duniya wato WFP da Asusun tallafawa kanannan yara na Majalisar dinkin Duniya UNICEF, Gidanuniyar Kula da kananan Yara da kuma kungiyar Kare Raji ta Mercy Corps, sun jima suna jaddada mahimmancin daukar matakan gaggawa na jin kai kafin aukuwar dukkanin wata annoba.
Daga cikin sakamkon taro na CH da aka gudaanr a Abuja wakilin FOA Nijeriya Kouacoau Dominikue Koffy ya jabawa Gwamnatin Tarayya da kuma masu ruwa da tsaki a CH, musamman bisa mayar da hankali da suka yi wajen ganin an samar da wadataccen abinci da kuma sanya ido da suke yi don a samar da wadataccen abincin.
Ya kuma yi kira ga Gwamnatocin Jihohi da sauran abokan hadaka da su zuba kudade domin a wanzar da tsarin na kasa da a za a gudanar a watan Okotobar 2025, inda ya yi nuni da cewa, ba tare da an samar da bayanai da samar da kyakyanwan shiri zai yi wuya, a cimma burin da aka sanya a gaba.
A ra’ayin wannan jaridar, mun yi amannar cewa, kalubalen karancin abinci abu ne da ke bukatar hada karfi da karfe, wanda hakan zai wuce batun siyasantar da maganar da shelanta samar da Rumbunan adana hatsi.
Ya zama wajibi Gwamnatin Tarayya ta ayyana dokar ta vaci wajen samar da wadataccen abinci tare da kafa tawaga mai karfi da za ta hada da Ma’aikatun Gwamnati, Hukumomin Tsaro, kungiyoyin Jin kai, Kamfanonin Masu Zaman Kansu da sauran masu ruwa da tsaki, musamman domin a samar da tare da kaddamar da kyakyawan tsari na kasa.
Dole ne Gwamnatocin Jihohi su marawa kokarin da Gwamnatin Tarayya ke yi kan zuba nannun jari wajen samar da abinci, samar da kayan adana amfanin gona, tsarin rabar da amafnin gonar, kuma kamfanoni masu zaman kansu, musamman masu yin noma domin samun riba, suma suna da gudunmawr da za su bayar wajen kara bunkasa fannin aikin noma, musamman domina a tabbatar da cewa, abincin ya isa ga teburin, musamman marasa karfi, wadanda kuma za su rinka sayen abincin, a cikin farashi mai sauki.
Ya zama wajbi UNICEF, FAO, WEF, da sauran takwarororin su, da su kara kaimi wajen aikin sa kai a yankunan da karancin abinci ya fi kamari, domin taimakawa Gwamnati wajen wanzar da aikin na dogon zango.
A zaman mu na kasa, ba ta savu mu yi ikirarin cewa, kasar na kan turba ba, bayan alhali, ‘yan kasar na ci gaba da fuskantar yunwa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp