Na gaji bashin 8.9bn a matsayin shugaban APC — Ganduje
Published: 26th, February 2025 GMT
Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa shugabancinsa ya gaji bashin Naira biliyan 8.9.
Ganduje ya bayyana haka ne a Abuja yayin taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na jam’iyyar APC.
Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno Buhari da El-Rufai ba su halarci babban taron APC baA cewarsa, wannan bashi ya samo asali ne daga kuɗaɗen da aka kashe a shari’o’i kafin zaɓe, ƙalubalantar sakamakon zaɓe, da ƙarar da aka shigar da ’yan majalisu, gwamnoni, da na shugaban ƙasa.
“Shugabancin kwamitin zartaswa na ƙasa na yanzu ya gaji bashin Naira 8,987,874,663 da kuma tari shari’o’i daban-daban,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa mai bai wa jam’iyyar shawara kan harkokin shari’a, Farfesa Abdul Kareem Kana (SAN), na aiki don rage wannan bashi.
“Muna sake roƙon Kwamitin Zartarwa na Ƙasa da ya taimaka domin shawo kan matsalar,” in ji Ganduje.
Taron ya samu halartar Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, Mataimakinsa Kashim Shettima, Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, gwamnonin jihohi da wasu manyan shugabannin jam’iyyar.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta yanke wa tsohon Shugaban Peru ɗaurin shekaru 15 kan laifin rashawa
An yanke wa tsohon shugabar ƙasar Peru, Ollanta Humala hukuncin daurin shekaru 15 a gidan yari.
Wata kotu a ƙasar ce ta yanke masa hukuncin bisa samunsa da laifin halatta kuɗin haram a badaƙalar cin hanci da katafaren kamfanin gine-gine na Brazil Odebrecht ke yi don samun kwangila.
Dalilin da Kwankwaso zai dawo APC — Ganduje Gwamnatin Tarayya ta ayyana hutu ranar Juma’a da LitininHaka kuma, ita ma mai ɗakinsa, Nadine Heredia, an yanke mata makamancin wannan hukuncin, duk da cewa ba ta halarci zaman kotun ba, saboda haka alƙalin ya bayar da umarnin kamo ta.
Ollanta Humala, mai shekaru 62, ya kasance tsohon shugaban ƙasar Peru na biyu da aka samu da laifi, lamarin da ya sa nan take aka kai shi wani gidan yari da ke gabashin Lima, inda ake tsare da tsoffin shugabannin kasar Peru Alejandro Toledo da Pedro Castillo.
Wannan hukuncin na zuwa ne sama da shekaru uku da fara shari’ar Humala wanda ya mulki ƙasar Peru daga 2011 zuwa 2016 —amma dai lauyoyinsa sun bayanna cewa za su ɗaukaka ƙara.
Ma’aikatar Shari’a ta Amurka ta ce Kamfanin Odebrecht ya ba da cin hanci dala miliyan 788 a cikin shekaru goma ga gwamnatocin yankin Latin Amurka domin samun kwangilar gine-gine.
Kamfanin ya bayyana cewar ya bayar da dala miliyan 29 na cin hanci ga Peru a tsakanin 2005 da 2014.