Na gaji bashin 8.9bn a matsayin shugaban APC — Ganduje
Published: 26th, February 2025 GMT
Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa shugabancinsa ya gaji bashin Naira biliyan 8.9.
Ganduje ya bayyana haka ne a Abuja yayin taron Kwamitin Zartarwa na Ƙasa (NEC) na jam’iyyar APC.
Boko Haram sun sace mutum 2 da kayan abinci a Borno Buhari da El-Rufai ba su halarci babban taron APC baA cewarsa, wannan bashi ya samo asali ne daga kuɗaɗen da aka kashe a shari’o’i kafin zaɓe, ƙalubalantar sakamakon zaɓe, da ƙarar da aka shigar da ’yan majalisu, gwamnoni, da na shugaban ƙasa.
“Shugabancin kwamitin zartaswa na ƙasa na yanzu ya gaji bashin Naira 8,987,874,663 da kuma tari shari’o’i daban-daban,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa mai bai wa jam’iyyar shawara kan harkokin shari’a, Farfesa Abdul Kareem Kana (SAN), na aiki don rage wannan bashi.
“Muna sake roƙon Kwamitin Zartarwa na Ƙasa da ya taimaka domin shawo kan matsalar,” in ji Ganduje.
Taron ya samu halartar Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, Mataimakinsa Kashim Shettima, Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, gwamnonin jihohi da wasu manyan shugabannin jam’iyyar.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Nijar : An nada Janar Tiani, a mukamin shugaban rikon kwarya
A Jamhuriyar Nijar, an daga martabar Abdourahmane Tiani madugun juyin mulkin sojin kasar daga mukamin Birgediya Janar zuwa Janar, mukamin soji mafi girma a kasar.
An ba Abdourahmane Tiani wannan mukamin ne bayan tabbatar masa da mukamin shugaban rikon kwarya na kasar a bikin da aka gudanar a jiya Laraba a Yamai babban birrin kasar.
Kafin hakan kuma Janar Abdourahamane Tiani, ya sa hannu kan dokar tsarin mulki na wucin gadi, mai taken “Tsarin farfado da Nijar”.
Bisa wannan doka, Tiani zai jagoranci kasar tsawon shekaru 5 tun daga ranar kaddamar da dokar, yayin da ainihin wa’adinta zai danganta da halin tsaro, da bukatun farfadowar kasar, da kuma ajandar kawancen kasashen Nijar da Mali da Burkina Faso.
Hukumomin wucin gadin sun kunshi shugaban jamhuriyar Nijar, da kwamiti mai kula da harkokin tsaron kasar, da gwamnati da kwamitin sulhu, da hukumar sa ido kan harkar jin kai da sauransu.
Wata dokar kuma da shugaban rikon kwaryar ya sanya wa hannu a jiya ita ce ta rusa dukkanin jam’iyyun siyasa a duk fadin kasar.
An amince da wannan sabon tsarin mulki ne bisa kudurorin da aka tattara, a yayin taron farfado da kasa da aka gudanar a tsakanin ranakun 15 zuwa 19 ga watan da ya gabata a birnin Yamai, fadar mulkin kasar.