Kwanan nan, mamban hukumar siyasa na kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin wato JKS, kuma sakatarorin sakatariyar hukumar, da mamban kungiyar JKS na zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin NPC, majalisar gudanarwa kuma majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin CPPCC, da kuma darektan kwamitin JKS na kotun jama’a ta koli kuma hukumar gabatar da kararraki ta koli, sun ba da rahotannin tantance nasarorin aiki ga kwamitin kolin JKS da kuma babban sakatarensa Xi Jinping.

Xi ya duba rahotannin kuma ya gabatar da muhimman bukatu. Yana mai jaddada cewa, shekarar bana ita ce shekarar karshe ta shirin shekaru biyar-biyar na 14, kuma muhimmiyar shekara ce ta kara zurfafa yin gyare gyare. Dole ne a mai da hankali cikin natsuwa game da kalubalen da sauye-sauyen yanayi na cikin gida da na waje suka haifar, da tabbatar da ingantaccen ci gaba, da habaka bude kofa ga waje a babban mataki, da inganta rayuwar jama’a a kai a kai. Dole ne mu dauki sabbin nauyi kuma mu yi sabbin ayyuka a sabuwar tafiya ta inganta zamanantarwa irin ta kasar Sin. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ta kasar Sin

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙungiya ta rage farashin kayan marmari saboda Azumin Ramadan

Shugaban Kungiyar ’Yan Kasuwa Masu Hada-hadar Kayan Marmari a Jihar Oyo, Walin Ibadan, Alhaji Dauda Shehu ya ce, kungiyar za ta rage farashin kayan marmari domin samun sauƙi ga al’ummar Musulmi a cikin watan Azumin Ramadan.

Ya ce, “kamar yadda muka saba yi a baya a irin wannan lokaci, a bana ma za mu rage farashin kayan marmari kamar dankalin Turawa da karas da kukumba da latas da koren tattasai da ake fataucin su daga wasu jihohin Arewa zuwa Kudancin kasa.

Ahmed Musa ya buƙaci a gudanar da bincike kan mutuwar ɗan wasan Nijeriya a Uganda Mayaƙan Boko Haram sun sace kwale-kwale 8 a Borno

“Za mu yi ragin ne daidai gwargwado daga cikin ribar da muke samu saboda albarkar wannan wata’’, inji shi.

Da yake zagayawa da Aminiya sassa daban-daban na kasuwar kayan marmari ta Benjamin da ke Eleyele a Ibadan babban birnin Jihar Oyo, Alhaji Dauda Shehu ya ce, mun yi wata ganawa ta musamman a tsakaninmu da ’yan kasuwa masu fataucin irin wannan kaya daga jihohin Filato da Kaduna da Kano da Sakkwato.

Ya ce sun amince da yi wa kansu da al’ummar Musulmi adalci wajen sauko da farashin kayan a cikin kwana 30 na watan Azumin Ramadan, domin saukaka wa Musulmi da rage masu radadin tsadar rayuwa a wannan lokaci.

Sai dai ya ce, farashin wadannan kaya za su koma yadda ake sayar da su a baya da zarar watan Azumin ya kare.

Ya ce, “mun yi hakan ne saboda albarkar wannan wata na Ramadan, amma bayan kammala kwana 30 na watan Azumin, ya zama wajibi mu mayar da farashin wannan kaya kamar yadda muke sayarwa a baya domin ci gaba da rage farashin zai iya janyo mana asara.

“Muna daukar matakin rage farashin kayan ne bayan mun rage ribar da ke shiga aljihunmu.

Da yake amsa wata tambaya, Alhaji Dauda Shehu ya ce, “masu sarin irin wannan kaya daga sashen Kudu maso Yamma da suke rububin shigowa cikin wannan kasuwa ta Ibadan a kowane garin Allah Ya waye, mun ba su shawarar daukar matakin rage farashin kayan a garuruwan da suka fito, domin samun sauki ga Musulmi a cikin wannan lokaci.

Ya ce, “tashin farashin irin wannan kaya ba laifin mu ba ne, domin yanayi ne da ya shafi kasa baki daya da ke matukar bukatar ci gaba da addu’o’in rokon Allah samun sauki.”

Alhaji Dauda Shehu ya ce, a yanzu haka ana sauke nau’in irin wannan kaya a cikin manyan motoci uku zuwa biyar a kullum a cikin kasuwar ta Benjamin, inda manya da kananan ’yan kasuwa suke rububin saye domin baje-kolinsu a cikin shagunan cikin gari da masu yawon talla a kan hanyoyin birnin na Ibadan.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sheikh Na’im Kasim Ya Gana Da Ministan Harkokin wajen Kasar Iran Da Shugaban Majalisar Dokoki
  • Wakilin Sin: Dole Ne A Aiwatar Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Gaza
  • Ƙungiya ta rage farashin kayan marmari saboda Azumin Ramadan
  • MDD : Kwamitin Sulhu ya amince da kudurin Amurka kan rikicin Rasha da Ukrain
  • Ya Kamata Trump Ya Yi Koyi Da Nixon
  • Hukumar NPC Za Ta Gudanar Da Kidayar Jama’a Cikin Aminci- Shugaba Tinubu
  • Iran A Karon Farko Ta Gwada Aiki Da Sabbin Jiragen Yakin Da Ta Kera A Cikin Atisayen Zulfikar da Ke Gudana A Halin Yanzu
  • Gwamnatin Iraki Ta Kokawa Sabuwar Gwamnatin Siriya Dangane Da Barazanar Mayakan Daesh Da Suka Rage A Kasar
  • Kasar Sin Ta Zayyana Muhimman Ayyukanta Na Zurfafa Gyare-gyare A Yankunan Karkara Da Inganta Raya Su